Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranar Alhamis, 1 ga watan Oktoba, a matsayin ranar hutu domin bikin cikar kasarnan shekaru 60 da samun yancin kai.
Ministan harkokin cikin gida, Rauf Aregbesola, ya ayyana hutun a madadin gwamnatin tarayya.
Babbar sakatariya a ma’aikatar cikin gida, Georgina Ehuriah, ta sanar da haka cikin wata sanarwar da ta fitar yau a Abuja.
- Gwamnatin Sokoto Ta Bai Wa Sojojin Najeriya Gudummuwar Motocin Sulke 62
- Guguwar Iska Ta Kashe Mutane Uku, Ta Lalata Gidaje Da Ababen More Rayuwa A Yobe
- Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Takwas, Sun Kwato Makamai A Katsina
- Gwamnan Zamfara: Na Ƙi Biyan Kuɗin Fansa Naira Miliyan 300, Na Ce Su Kashe ‘Yan Uwana
- EFCC Ta Gurfanar da Bello Bodejo Kan Zargin Badaƙalar Kuɗi
Aregbesola ya taya daukacin yan Najeriya murnar cikar kasarnan shekaru 60 da yancin kai, inda ya tabbatar musu da jajircewar gwamnatin wajen habaka jin dadi da tattalin arzikin kasarnan.
Da yake taya yan Najeriya murna gudanar da bukukuwan yancin kan lafiya, ministan ya tunatar da cewa wadanda suka kwatowa kasarnan yanci, duk da banbancin addini, kabila da yare, sun hada kan su domin samun yancin kan kasa.