Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranar Alhamis, 1 ga watan Oktoba, a matsayin ranar hutu domin bikin cikar kasarnan shekaru 60 da samun yancin kai.
Ministan harkokin cikin gida, Rauf Aregbesola, ya ayyana hutun a madadin gwamnatin tarayya.
Babbar sakatariya a ma’aikatar cikin gida, Georgina Ehuriah, ta sanar da haka cikin wata sanarwar da ta fitar yau a Abuja.
- Airtel ta dakatar da bayar da bashin kati da data a Najeriya
- ’Yan adawa ba su isa su razanar da ni ba – Tinubu
- Sojoji sun kama masu satar man fetur a Legas, sun kama mutum 14
- Talauci ya ragu daga kaso 91 zuwa 41 a jihar Sokoto
- Bayan shekaru 12 da sace ɗaliban Chibok 272, har yanzu ba a san makomar 83 ba
Aregbesola ya taya daukacin yan Najeriya murnar cikar kasarnan shekaru 60 da yancin kai, inda ya tabbatar musu da jajircewar gwamnatin wajen habaka jin dadi da tattalin arzikin kasarnan.
Da yake taya yan Najeriya murna gudanar da bukukuwan yancin kan lafiya, ministan ya tunatar da cewa wadanda suka kwatowa kasarnan yanci, duk da banbancin addini, kabila da yare, sun hada kan su domin samun yancin kan kasa.