Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranar Alhamis, 1 ga watan Oktoba, a matsayin ranar hutu domin bikin cikar kasarnan shekaru 60 da samun yancin kai.
Ministan harkokin cikin gida, Rauf Aregbesola, ya ayyana hutun a madadin gwamnatin tarayya.
Babbar sakatariya a ma’aikatar cikin gida, Georgina Ehuriah, ta sanar da haka cikin wata sanarwar da ta fitar yau a Abuja.
- An miƙa wa hukumar INEC ƙorafin yi wa Sanata Natasha kiranye
- An kama masu zanga-zanga 1,133 a Turkiyya cikin kwana biyar
- Ba lallai ba ne haɗakar ƴan siyasar Najeriya ta yi tasiri – Shekarau
- Fursunoni 12 sun tsere daga gidan yari a jihar Kogi
- An kama mutum 12 bisa zargin kashe wani matashi a masallaci a jihar Kaduna
Aregbesola ya taya daukacin yan Najeriya murnar cikar kasarnan shekaru 60 da yancin kai, inda ya tabbatar musu da jajircewar gwamnatin wajen habaka jin dadi da tattalin arzikin kasarnan.
Da yake taya yan Najeriya murna gudanar da bukukuwan yancin kan lafiya, ministan ya tunatar da cewa wadanda suka kwatowa kasarnan yanci, duk da banbancin addini, kabila da yare, sun hada kan su domin samun yancin kan kasa.