

Mai Martaba sarkin dutse Dr. Nuhu muhammad Sanusi ya bukaci gwamnatin tarayya data taimaka wajen yashe madatsun ruwan da ake dasu a fadin kasar nan.
Mai Martaba Sarki ya yi wannan kiran ne lokacin da Gwamna Muhammad Badaru Abubakar ya kai masa ziyarar jaje dangane da mutanen da suka gamu da ambaliyar ruwa a masarautar Dutse.

Nuhu Muhammadu Sanusi ya ce fiye da shekaru 50 ke nan ba’a yashe madatsun ruwa na Tiga da Chalawa ba, wanda hakan ke jawo ambaliyar ruwa duk shekara dake lalata gonaki da rushe gidaje.
- Tarihin Gamuwa 10 Tsakanin Kano Pillars VS Eyimba Da Kuma Wasan Yau
- Abubuwa 5 da suka zama wajibi lokacin sanyi
- An ƙaddamar da kudin kariya ga ƴan jarida da masu fafutukar ƴancin amfani da yanar gizo
- Yadda ake duba suna don zama ma’aikacin damara na 2020 a Nijeria
- Me Ƙungiyar Izala ta ce kan matsalolin tsaro a Najeriya?
Mai Martaba Sarkin Dutse ya ce ambaliyar ruwa da ta faru a jihar Jigawa ta fi karfin gwamnatin jiha dan haka akwai bukatar gwamnatin tarayya ta shigo cikin wannan lamari.
Tun da farko, Gwamna Muhammad Badaru Abubakar yace ya ziyarci fardar sarkin ne a cigaba da ziyarar masu Martaba sarakunan jiharnan domin jajanta musu dangane da iftila’in ambaliyar ruwa data samu al’ummomin su.