Mai Martaba sarkin dutse Dr. Nuhu muhammad Sanusi ya bukaci gwamnatin tarayya data taimaka wajen yashe madatsun ruwan da ake dasu a fadin kasar nan.
Mai Martaba Sarki ya yi wannan kiran ne lokacin da Gwamna Muhammad Badaru Abubakar ya kai masa ziyarar jaje dangane da mutanen da suka gamu da ambaliyar ruwa a masarautar Dutse.
Nuhu Muhammadu Sanusi ya ce fiye da shekaru 50 ke nan ba’a yashe madatsun ruwa na Tiga da Chalawa ba, wanda hakan ke jawo ambaliyar ruwa duk shekara dake lalata gonaki da rushe gidaje.
- Al’ummar Indiya sun fara kaɗa kuri’a a zaɓen da aka kasa gida bakwai cikin makonni shida
- Jami’an ‘yan sanda a Katsina sun dakile wani hari da aka kai garin Sabuwa dake jihar
- Rundunar sojin Najeriya ba za ta tsagaita ba wajen kawar da masu aikata miyagun laifuka
- Shugaba Bola Tinubu ya amince da wasu tsare-tsare guda uku don inganta fannin ilimi a kasar nan
- Gwamnatin jihar Nasarawa ta dakatar da duk wata Ƙungiyar ’yan banga a jihar
Mai Martaba Sarkin Dutse ya ce ambaliyar ruwa da ta faru a jihar Jigawa ta fi karfin gwamnatin jiha dan haka akwai bukatar gwamnatin tarayya ta shigo cikin wannan lamari.
Tun da farko, Gwamna Muhammad Badaru Abubakar yace ya ziyarci fardar sarkin ne a cigaba da ziyarar masu Martaba sarakunan jiharnan domin jajanta musu dangane da iftila’in ambaliyar ruwa data samu al’ummomin su.