Hukumar bada agajin gaggawa ta jihar jigawa ta tabbatar da mutuwar akalla mutane 40 a fadin jiharnan inda tace dubbun mutane ne suka tserewa muhallinsu da asarar gonakinsu sanadiyyar iftila’in amballiyar ruwa.
Shugaban hukumar Sani Ya’u Babura wanda ya tabbatar da mutuwar mutanen, yace hukumar su ta kammala tattara duk wani bayanai da zata turawa jami’anta domin bayar da agajin gaggawa ga wadanda iftala’in ya afkawa.
- Gwamnan jihar Kogi ya nemi gwamnatin tarayya da ta taimakawa jihar wajen yaki da matsalar tsaro da ambaliyar ruwa
- An kama wasu mutane biyu da ake zargi da laifin fasa kwaurin wutar lantarki a jihar Katsina
- Hukumar Kwastam ta kama shinkafar kasar waje guda 212 wanda kudinsu ya haura N126m
- Daniel Bwala mai magana da yawun Atiku Abubakar ya caccaki Hukumar EFCC
- An kama wasu masu garkuwa da mutane uku a yankin Lankaviri dake jihar Taraba
Sani Babura ya kara da cewa sunyi kokari sosai wajan tattara adadin mutanen da suka rasa rayukansu, gonakinsu da wadanda suka tserewa muhallinsu.
Ya kara da cewa baya ga haka, Gwamnatin jihar jigawa na bukatar taimakon hukumar bada agajin gaggawa ta kasa NEMA.