Hukumar bada agajin gaggawa ta jihar jigawa ta tabbatar da mutuwar akalla mutane 40 a fadin jiharnan inda tace dubbun mutane ne suka tserewa muhallinsu da asarar gonakinsu sanadiyyar iftila’in amballiyar ruwa.
Shugaban hukumar Sani Ya’u Babura wanda ya tabbatar da mutuwar mutanen, yace hukumar su ta kammala tattara duk wani bayanai da zata turawa jami’anta domin bayar da agajin gaggawa ga wadanda iftala’in ya afkawa.
- Airtel ta dakatar da bayar da bashin kati da data a Najeriya
- ’Yan adawa ba su isa su razanar da ni ba – Tinubu
- Sojoji sun kama masu satar man fetur a Legas, sun kama mutum 14
- Talauci ya ragu daga kaso 91 zuwa 41 a jihar Sokoto
- Bayan shekaru 12 da sace ɗaliban Chibok 272, har yanzu ba a san makomar 83 ba
Sani Babura ya kara da cewa sunyi kokari sosai wajan tattara adadin mutanen da suka rasa rayukansu, gonakinsu da wadanda suka tserewa muhallinsu.

Ya kara da cewa baya ga haka, Gwamnatin jihar jigawa na bukatar taimakon hukumar bada agajin gaggawa ta kasa NEMA.