

Hukumar bada agajin gaggawa ta jihar jigawa ta tabbatar da mutuwar akalla mutane 40 a fadin jiharnan inda tace dubbun mutane ne suka tserewa muhallinsu da asarar gonakinsu sanadiyyar iftila’in amballiyar ruwa.
Shugaban hukumar Sani Ya’u Babura wanda ya tabbatar da mutuwar mutanen, yace hukumar su ta kammala tattara duk wani bayanai da zata turawa jami’anta domin bayar da agajin gaggawa ga wadanda iftala’in ya afkawa.
- Kuji tsoron Allah ko koma gare Shi, Atiku yayi kira ga yan Najeriya.
- Goodluck Jonathan: Kuri’un talakawa ya kamata su tattance zabe ba kotu ba
- Sarkin musulmi: Gobe Talata shine daya ga watan Ramadan
- Kamfanin Twitter zai kafa reshe a Afirka
- Kungiyar Barcelona ta fi ko wacce kungiya kudi a duniya
Sani Babura ya kara da cewa sunyi kokari sosai wajan tattara adadin mutanen da suka rasa rayukansu, gonakinsu da wadanda suka tserewa muhallinsu.

Ya kara da cewa baya ga haka, Gwamnatin jihar jigawa na bukatar taimakon hukumar bada agajin gaggawa ta kasa NEMA.