Kungiyyar cigaban masarautar Hadejia (HEDA) ta dora alhakin ambaliyyar ruwan da ke faruwa akan gwamnatocin yanzu da na baya na tarayya da jiha.
Masarautar dake yankin arewa maso gabas na jihar Jigawa, tana da kananan hukumomi 8 a karkashinta, wadanda suka hada da Hadejia, Kaugama, Auyo, Malammadori, Birniwa, Guri, Kirikasamma and Kafin Hausa.

Shugaban kungiyyar , Abdullah Sarki Kafinta, wanda ya zanta da manema labarai anan cikin garin Hadejia, ya bayyana takaicin sa kan yadda al’ummar cikin garin Hadejia suka rasa kadarorinsu, gidaje da rayukansu sanadiyyar ambaliyyar ruwan.
- Gwamnatin Sokoto Ta Bai Wa Sojojin Najeriya Gudummuwar Motocin Sulke 62
- Guguwar Iska Ta Kashe Mutane Uku, Ta Lalata Gidaje Da Ababen More Rayuwa A Yobe
- Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Takwas, Sun Kwato Makamai A Katsina
- Gwamnan Zamfara: Na Ƙi Biyan Kuɗin Fansa Naira Miliyan 300, Na Ce Su Kashe ‘Yan Uwana
- EFCC Ta Gurfanar da Bello Bodejo Kan Zargin Badaƙalar Kuɗi
Sannan yayi kira ga gwamnatin tarayya da taimakawa al’ummar yankin da irin shuka daban daban da irin kifi daza a zuba a kududdufai idan ambaliyyar ruwan ta wuce.