Hukumar kula da wutar lantarki ta kasa a jiya ta umarci kamfanonin rarraba wutar lantarki 11 dasu dakatar da karbar sabon kudin wuta wanda suka fara a ranar 1 ga watan Satumba, na tsawon makonni biyu.
Umarnin dakatarwar dauke da kwanan watan 28 ga watan Satumba, na dauke da sa hannun shugaban hukumar, James Momoh, tare da kwamishinan shari’ah lasisi da bin umarni, Dafe Akpeneye.
- Muna bincike kan Gwamnoni guda 18 da ke kan mulki – Shugaban EFCC
- Tinubu ya kafa kamfanin zuba jari da raya yankin Kudu maso Gabas tare da zuba jarin farko na Naira Biliyan 150 don soma aiki
- ‘Yan sanda sun tabbatar da mutuwar malamin Jami’ar Prince Abubakar Audu da ke Jihar Kogi yayin da yake lalata da wata daliba a ɗakin otel, bayan shan maganin ƙarfafa maza a karo na biyu.
- Ganduje na hutu ne da wasu uzurai a Landan tare da iyalansa bayan barin sa ofis a matsayin Shugaban Jam’iyya In ji Muhammad Garba
- An sake mayar da ’yan Najeriya 294 gida daga Jamhuriyar Nijar a makon nan in ji NEMA
Hukumar tace umarnin dakatarwar za tayi aiki daga ranar 28 ga watan Satumba zuwa 11 ga watan Oktoba, lokacin da zata kare.
A ranar 1 ga watan Satumba, hukuma ta amince da sabon kudin wata na bana domin kamfanonin rarraba wutar lantarki 11.
Biyo bayan amincewa da sabon kudin wutar da hukumar ta yi, nan take kamfanonin rarraba wutar lantarki suka kara kudaden wutarsu, wanda kawo yanzu ake karba tsawon makonni hudu.