Jam’iyyar PDP za ta gudanar da babban taronta a jihohi 25 domin zaben sabbin shugabanni

0 123

Jam’iyyar PDP za ta gudanar da babban taronta a jihohi 25 domin zaben sabbin shugabanni da sauran mambobin zartaswa.

Sakataren kungiyar na kasa Umar Bature ne ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da manema labarai.

Jihohin da abin ya shafa sun hada da Edo, Akwa Ibom, Bayelsa, Cross River, Delta, Rivers, Kano, Kaduna, Katsina, Sokoto, Jigawa, Niger, Benue, Nasarawa, Gombe, Enugu, Imo, Abia, Ondo, Ekiti da kuma babban birnin tarayya Abuja. ,

Kwamitin ayyuka na jam’iyyar na kasa ya yi wani taro a ranar 26 ga Maris a Abuja, ya ce yana tantance wa’adin shugabannin jihohi 26 da wa’adinsu ya kare.

A wata sanarwa da sakataren yada labaran jam’iyyar na kasa, Debo Ologunagba ya fitar, PDP ta bayyana cewa kwamitocin riko da aka kafa a jihohi 21 za su kula da al’amuran jam’iyyar na tsawon watanni uku.

Leave a Reply

%d bloggers like this: