Sanata Ibrahim Hassan ya kai agaji ga wadanda ambaliya ta shafa
A nan jihar Jigawa, yayinda al’umma ke cikin halin damuwa sakamakon ifti’la’in ambaliyar ruwa da tayi sanadin muhallai da gonakinsu, a kokarin saukaka radadin zukata, sanatan jihar mai wakiltar santoriyar gabas Barrister Ibrahim Hassan, ya bayar da gudun mawar kayayyakin tallafi ga wadanda abin ya shafa a karamar hukumar Kriskasamma.
Da yake mika kayayyakin a madadin Sanatan, shugaban kungiyar yan kasuwar masarautar Hadejia Alhaji Idris Maji Dadin Jabo, yace kayayyakin sun kunshi fatun buhu 100, buhunan gari 5, buhun sukari 2 da kuma tabarmi 120.
- Gwamnatin Jigawa ta jadadda kudirinta na daukar kwararan matakai na rage talauci a jihar
- An kama haramtattun nakiyoyi 6,240 a hanyar Yauri zuwa Jega da ke Jihar Kebbi
- Gwamnati na shirin farfado da masaku da nufin bunkasa noman auduga da samar da tufafi
- Hukumomi na aiki da jami’an tsaro wajen kamo duka ragowar fursunoni 109 da suka tsere daga gidan gyaran hali
- Za’a gudanar da cikakken bincike don tabbatar da ingancin duka jiragen sama da ke zirga-zirga a Najeriya
Da yake karbar kayayyakin, shugaban karamar hukumar Alhaji Salisu Garba Kubayo, ya yaba da kokarin sanatan, tare da alkauranta rabon kayan a fadin mazabun karamar hukumar 5.
Saurari hirar da wakilinmu yayi da Sanatan da kuma bubuwa da ya fada