A nan jihar Jigawa, yayinda al’umma ke cikin halin damuwa sakamakon ifti’la’in ambaliyar ruwa da tayi sanadin muhallai da gonakinsu, a kokarin saukaka radadin zukata, sanatan jihar mai wakiltar santoriyar gabas Barrister Ibrahim Hassan, ya bayar da gudun mawar kayayyakin tallafi ga wadanda abin ya shafa a karamar hukumar Kriskasamma.
Da yake mika kayayyakin a madadin Sanatan, shugaban kungiyar yan kasuwar masarautar Hadejia Alhaji Idris Maji Dadin Jabo, yace kayayyakin sun kunshi fatun buhu 100, buhunan gari 5, buhun sukari 2 da kuma tabarmi 120.
- Gwamnatin Sokoto Ta Bai Wa Sojojin Najeriya Gudummuwar Motocin Sulke 62
- Guguwar Iska Ta Kashe Mutane Uku, Ta Lalata Gidaje Da Ababen More Rayuwa A Yobe
- Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Takwas, Sun Kwato Makamai A Katsina
- Gwamnan Zamfara: Na Ƙi Biyan Kuɗin Fansa Naira Miliyan 300, Na Ce Su Kashe ‘Yan Uwana
- EFCC Ta Gurfanar da Bello Bodejo Kan Zargin Badaƙalar Kuɗi
Da yake karbar kayayyakin, shugaban karamar hukumar Alhaji Salisu Garba Kubayo, ya yaba da kokarin sanatan, tare da alkauranta rabon kayan a fadin mazabun karamar hukumar 5.
Saurari hirar da wakilinmu yayi da Sanatan da kuma bubuwa da ya fada