Gwamnan babban bankin kasa CBN Mr. Godwin Emefiele, yace za’a dauki matakin fadada wasu ka’idoji da nufin shawo kan karayar tattalin arziki, kasancewar ka’idojin dake akwai a yanzu haka sun kuntata.
Ya bayyana hakan a matsayin tilas domin shawo kan durkushewar tattalin arziki da kuma karancin wadatuwar takardun kudade a hannun jama’a, matakin da kwamatin tsare tsaren kudade na bankin ya cimma a taron da ya gudanar makon jiya.
- Airtel ta dakatar da bayar da bashin kati da data a Najeriya
- ’Yan adawa ba su isa su razanar da ni ba – Tinubu
- Sojoji sun kama masu satar man fetur a Legas, sun kama mutum 14
- Talauci ya ragu daga kaso 91 zuwa 41 a jihar Sokoto
- Bayan shekaru 12 da sace ɗaliban Chibok 272, har yanzu ba a san makomar 83 ba
Emmefiele ya alakanta hakan da janye tallafin mai na baya bayannan, da ya haddasa hauhauwar farashinsa, da kuma kwaskwarima da da akayiwa kasuwar canjin kudi, wanda yace muddin ba’a dauki matakan da suka kamata ba, to babu shakka kalubaken karancin takardun kudaden zai tsaurara.