Karanta matakin da gwamnatin tarayya take shirin bullowa da shi don rage matsatsi
Gwamnan babban bankin kasa CBN Mr. Godwin Emefiele, yace za’a dauki matakin fadada wasu ka’idoji da nufin shawo kan karayar tattalin arziki, kasancewar ka’idojin dake akwai a yanzu haka sun kuntata.
Ya bayyana hakan a matsayin tilas domin shawo kan durkushewar tattalin arziki da kuma karancin wadatuwar takardun kudade a hannun jama’a, matakin da kwamatin tsare tsaren kudade na bankin ya cimma a taron da ya gudanar makon jiya.
- Gwamnatin jihar Nasarawa ta dakatar da duk wata Ƙungiyar ’yan banga a jihar
- EFCC sun kai samame gidan tsohon gwamnan jihar Kogi Yahaya Bello da ke Abuja
- Kwamitin gudanarwa na jam’iyyar PDP a Najeriya ya bayyana goyon bayansa ga Umar Damagum
- MƊD za ta ƙaddamar da asusun neman taimako domin samar da kayan agaji ga Falasɗinawa a Gaza
- Gwamnan Jihar Jigawa ya nemi ma’aikatun jihar da su cimma yarjejjeniyar da jihar ta kulla da Ofishin FCDO
Emmefiele ya alakanta hakan da janye tallafin mai na baya bayannan, da ya haddasa hauhauwar farashinsa, da kuma kwaskwarima da da akayiwa kasuwar canjin kudi, wanda yace muddin ba’a dauki matakan da suka kamata ba, to babu shakka kalubaken karancin takardun kudaden zai tsaurara.