Gwamnan babban bankin kasa CBN Mr. Godwin Emefiele, yace za’a dauki matakin fadada wasu ka’idoji da nufin shawo kan karayar tattalin arziki, kasancewar ka’idojin dake akwai a yanzu haka sun kuntata.
Ya bayyana hakan a matsayin tilas domin shawo kan durkushewar tattalin arziki da kuma karancin wadatuwar takardun kudade a hannun jama’a, matakin da kwamatin tsare tsaren kudade na bankin ya cimma a taron da ya gudanar makon jiya.
- Ronaldo ya yi alfahari da ɗansa ya buga wa Portugal tamaula
- Gwamna Uba Sani Ya Kafa Sabon Tarihi, Ya Yi Abin da ba a Taba Yi ba a Najeriya
- Tsohun gwamnan jihar Benue,ya baiyana cewa jam’iyyar PDP tana cikin mawuyacin hali da zai iya kai ta ga rushewa kafin 2027
- Sojoji masu mulkin Mali sun rusa dukkan jam’iyyun siyasa a kasar
- NiMET, ta fitar da sabon hasashen yanayi inda tace da yiwuwar ɓarkewar cututtukan ruwa a karshe shekara 2025
Emmefiele ya alakanta hakan da janye tallafin mai na baya bayannan, da ya haddasa hauhauwar farashinsa, da kuma kwaskwarima da da akayiwa kasuwar canjin kudi, wanda yace muddin ba’a dauki matakan da suka kamata ba, to babu shakka kalubaken karancin takardun kudaden zai tsaurara.