Ambaliya ta cinye wani sashe a jihar Borno

Mutane masu zama a unguwar Gomari Airport da ke Maiduguri, babban birnin Jihar Borno sun fice daga gidajensu kuma sun kwashe kayansu, bayan da ambaliya ta rutsa da gidajensu a ƙarshen makon da ya gabata na wannan watan na Yuli.

Majiyar mu tace wani shaida ya faɗa wa BBC Hausa cewa ambaliyar ta shafi unguwanni da dama a Maiduguri, ko da yake unguwar Gomari, na cikin wuraren da lamarin ya fi muni saboda kusancinsu da kogi.

Comments (0)
Add Comment