Hukumar gyaran hanyoyin mota ta kasa ta bada kwangilar gina gada a wani bangare na hanyar motar Hadejia zuwa Gamayin da ambaliyar ruwa ta lalata.
A jawabinsa wajen kaddamar da aikin a kauyen Wailare, jami’in shiyya na hukumar Injiniya Hussaini Abubakar yace an bada kwangilar ne ga kamfanin Dan Adida, kuma ana san kammalawa cikin watanni biyu masu zuwa.
- ‘Yan Bindiga Sun Sace Mai Unguwa Da Mata Hudu A Katsina
- Hukumar Makarantun Sakandaren Jigawa Ta Bude Tayin Kwangilar Motoci Da Kayan ICT
- Gwamnatin Jigawa Da UNICEF Za Su Horar Da ’Yan Mata 1,500 Sana’o’in Dogaro Da Kai
- Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Karɓi Buƙatar Gwamnatin Jihar Na Neman Amincewar Majalisar Domin Karɓar Bashin Naira Biliyan 84
- Ƴan Bindiga Sun Kai Hari A Kamaye, An Rasa Rayuka Da Jikkata Wasu
Yace Sanata Ibrahim Hassan Hadejia ne ya samo aikin bisa la’akari da muhimmancinsa ga tattalin arzikin jihohin Jigawa da Bauchi da Yobe da kuma Borno.
A sakonsa zuwa wajen bikin kaddamarwar, Gwamna Muhammad Badaru Abubakar, ta bakin mai bashi shawara na musamman akan ilimin gaba da sakandire, Muhammad T. Muhammad, yace bayar da kwangilar zai dafawa kokarin gwamnatin jihar na gyaran titunan da ambaliyar ruwa ta lalata a fadin jihar.