Hukumar gyaran hanyoyin mota ta kasa ta bada kwangilar gina gada a wani bangare na hanyar motar Hadejia zuwa Gamayin da ambaliyar ruwa ta lalata.
A jawabinsa wajen kaddamar da aikin a kauyen Wailare, jami’in shiyya na hukumar Injiniya Hussaini Abubakar yace an bada kwangilar ne ga kamfanin Dan Adida, kuma ana san kammalawa cikin watanni biyu masu zuwa.
- Gwamna Otu Ya Fadi Abubuwan da ke Janye Gwamnoni zuwa jam’iyar APC
- Atiku Abubakar yayi magana kan ficewar sa daga PDP
- Hukumar NEMA ta karɓi ‘yan Najeriya 203 da aka kwaso daga kasar Libya
- Kwamiti na jam’iyyar PDP ta yanke shawarar daukar matakin shari’a kan Sheriff Oborevwori
- Hukumar NDLEA ta yi nasarar kama kwayoyin da kudinsu ya haura naira biliyan 2.6 a Jihar Jigawa
Yace Sanata Ibrahim Hassan Hadejia ne ya samo aikin bisa la’akari da muhimmancinsa ga tattalin arzikin jihohin Jigawa da Bauchi da Yobe da kuma Borno.

A sakonsa zuwa wajen bikin kaddamarwar, Gwamna Muhammad Badaru Abubakar, ta bakin mai bashi shawara na musamman akan ilimin gaba da sakandire, Muhammad T. Muhammad, yace bayar da kwangilar zai dafawa kokarin gwamnatin jihar na gyaran titunan da ambaliyar ruwa ta lalata a fadin jihar.