Hukumar gyaran hanyoyin mota ta kasa ta bada kwangilar gina gada a wani bangare na hanyar motar Hadejia zuwa Gamayin da ambaliyar ruwa ta lalata.
A jawabinsa wajen kaddamar da aikin a kauyen Wailare, jami’in shiyya na hukumar Injiniya Hussaini Abubakar yace an bada kwangilar ne ga kamfanin Dan Adida, kuma ana san kammalawa cikin watanni biyu masu zuwa.
- Tsananin zafi yasa an rufe daukacin makarantun dake kasar Sudan ta kudu
- An sake sassauta dokar hana zirga-zirgar babura masu kafa uku a wasu sassan jihar Adamawa
- Sanata Abdul’Aziz Yari ya bukaci al’ummar Musulmi da su yi amfani da lokacin Ramadan wajen yi wa Shugaba Bola Tinubu addu’a
- Wasu ‘yan bindiga sun yi garkuwa da mutane 14 a kauyen Dogon Noma-Ungwan Gamo
- Dan majalisa mai wakiltar mazabar Kaga da Magumeri da Gubio a majalisar wakilai ya raba kayan abinci ga iyalai 5,000
Yace Sanata Ibrahim Hassan Hadejia ne ya samo aikin bisa la’akari da muhimmancinsa ga tattalin arzikin jihohin Jigawa da Bauchi da Yobe da kuma Borno.
A sakonsa zuwa wajen bikin kaddamarwar, Gwamna Muhammad Badaru Abubakar, ta bakin mai bashi shawara na musamman akan ilimin gaba da sakandire, Muhammad T. Muhammad, yace bayar da kwangilar zai dafawa kokarin gwamnatin jihar na gyaran titunan da ambaliyar ruwa ta lalata a fadin jihar.