Hukumar gyaran hanyoyin mota ta kasa ta bada kwangilar gina gada a wani bangare na hanyar motar Hadejia zuwa Gamayin da ambaliyar ruwa ta lalata.
A jawabinsa wajen kaddamar da aikin a kauyen Wailare, jami’in shiyya na hukumar Injiniya Hussaini Abubakar yace an bada kwangilar ne ga kamfanin Dan Adida, kuma ana san kammalawa cikin watanni biyu masu zuwa.
- An tsare wani mataimakin ministan tsaron kasar Rasha bisa zargin karbar cin hanci
- An dakatar da Daraktan kwalejin Birnin Kudu da jami’in kula da harkokin abinchi na kwalejin
- Gwamna Namadi yayi kira ga sabbin masu yiwa kasa hidima da aka turo jihar jigawa da su kasance jakadu na gari
- Majalisar dokokin jihar Jigawa ta kafa kwamatin wucin gadi domin nazari kan dokar hukumar zabe
- Jam’iyyar PDP za ta gudanar da babban taronta a jihohi 25 domin zaben sabbin shugabanni
Yace Sanata Ibrahim Hassan Hadejia ne ya samo aikin bisa la’akari da muhimmancinsa ga tattalin arzikin jihohin Jigawa da Bauchi da Yobe da kuma Borno.
A sakonsa zuwa wajen bikin kaddamarwar, Gwamna Muhammad Badaru Abubakar, ta bakin mai bashi shawara na musamman akan ilimin gaba da sakandire, Muhammad T. Muhammad, yace bayar da kwangilar zai dafawa kokarin gwamnatin jihar na gyaran titunan da ambaliyar ruwa ta lalata a fadin jihar.