Majalisar zartarwar jihar jigawa ta amince da kudi naira miliyan 330 domin samar da fitilun kan titi masu amfani da hasken rana a garuruwan Hadejia da Chai-Chai da Zandam da kuma Babura.
Kwamishinan yada labarai, matasa da wasanni, Bala Ibrahim Mamsa, ya sanar da hakan jim kadan bayan kammala taron majalissar da aka gudanar a gidan gwamnati dake Dutse.
Yace an bada kwangilar samar da fitilun kan titi masu amfani da hasken rana a garin Babura ga kamfanin Aren kan kudi naira miliyan 138, wanda za a kammala cikin watanni 3.
- ‘Yan bindiga sun kashe babban limamin masallacin Juma’a na kauyen Keita
- Gobara ta ƙone motoci da rumfunan katako takwas da kuma kayan aikin kafinta ƙurmus
- Kwamitin Masallacin Dutse ya raba buhunan Shinkafa buhu 30,000 ga zawarawa da sauran marasa galihu
- Kwamandojin Boko Haram biyu sun mika wuya ga sojojin rundunar hadin gwiwa ta MNJTF
- Dan takarar jam’iyyar adawa Bassirou Diomaye Faye ne ke kan gaba a zaben shugaban kasar Senegal
Majalisar ta kuma amince da bayar da kwangilar samar da fitilun kan titi masu amfani da hasken rana a nan Hadejia akan kudi naira miliyan 90, wanda ake sa ran kammalawa cikin watanni uku.
Ya kuma bayyana cewa an bayar da wani aikin samar da fitilun kan titi masu amfani da hasken rana a garin Chai-Chai na karamar hukumar Dutse da Zandam na Karamar Hukumar Gwaram.