Gwamnan Jigawa, Umar Namadi, ya jaddada aniyarsa ta ƙarfafa dimokuraɗiyya, tsaro da walwalar jama’a

0 364

Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, da takwaransa na Jihar Kebbi, Nasir Idris, sun jaddada aniyarsu ta ci gaba da inganta mulkin dimokuraɗiyya, tsaro da kuma jin daɗin al’umma a jihohinsu.

Gwamnonin sun bayyana hakan ne a saƙonnin taya murnar Ranar Dimokuraɗiyya ta 2026, inda suka yi bitar tafiyar dimokuraɗiyyar Najeriya tare da kira ga haɗin kai daga ‘yan ƙasa.

A nasa saƙon, Gwamna Namadi ya bayyana ranar 12 ga Yuni a matsayin muhimmiyar rana a tarihin Najeriya, wadda ke tunatar da irin gwagwarmayar da aka yi domin tabbatar da ‘yanci da adalci.

Ya ce dimokuraɗiyya ba kawai batun zaɓe ba ce, illa tana nufin gina cibiyoyi masu ƙarfi, tabbatar da bin doka, kare haƙƙin ‘yan ƙasa da kuma tabbatar da gaskiya a shugabanci.

Namadi ya ƙara da cewa gwamnatinsa ta mayar da hankali kan manyan fannoni kamar ilimi, lafiya, noma, ababen more rayuwa da tallafin jama’a marasa ƙarfi.

A nasa ɓangaren, Gwamna Nasir Idris ya yi kira ga ‘yan Najeriya da su kasance masu haƙuri, kishin ƙasa da bin doka, yana mai cewa dimokuraɗiyya na buƙatar haɗin kai da fahimtar juna.

Ya bukaci al’umma su guji duk wani abu da zai iya kawo rashin zaman lafiya, tare da goyon bayan hukumomin da ke da alhakin tsaro.

Duk gwamnonin sun kuma bayyana cewa gwamnatocinsu za su ci gaba da aiwatar da ayyukan ci gaba a fannoni daban-daban domin inganta rayuwar jama’a.

Sun kuma tabbatar da goyon bayansu ga shirin gwamnatin tarayya na Renewed Hope Agenda, tare da kira ga haɗin kai tsakanin matakai daban-daban na gwamnati.

Leave a Reply