An maka kamfanonin sadarwar wayar salula ƙara saboda rufe hanyoyin sadarwar a jihar Zamfara

Wata kungiyar farar hula mai suna Zamfara Circle, ta maka kamfanonin sadarwar wayar salula kara a gaban kotu tana neman a biya su diyyar naira miliyan 100 saboda rufe hanyoyin sadarwar wayar salula a jihar.

Kamfanonin MTN, Glo, 9mobile da kuma Airtel sune wadanda ake tuhuma a karar.

Gwamnan jihar Zamfara, Bello Matawalle, kwamishinan shari’a da kuma babban lauyan jihar da kuma hukumar sadarwa ta kasa (NCC) suna daga cikin wadanda ake tuhuma a karar.

Gwamna Matawalle ya bayar da umarnin dakatar da hanyoyin sadarwar wayar salula a jihar a wani mataki na magance matsalar rashin tsaro.

An dawo da hanyoyin sadarwar a wasu sassan jihar bayan an duba yanayin tsaro amma har yanzu kananan hukumomi shida ba su da hanyoyin sadarwar wayar hannu.

A karar da aka shigar a wata kotu da ke Gusau babban birnin jihar, kungiyar ta Zamfara Circle, ta ce rufe hanyoyin sadarwar ya jawo wahalhalu da asara ga masu amfani da wayoyin hannun.

Comments (0)
Add Comment