Majalisar zartarwar jihar Jigawa ta amince da bayar da kwangiloli wadanda kudinsu ya tasamma Naira biliyan daya da miliyan dari takwas a bangarorin ruwan sha da lafiya.
Tsohon kwamishinan yada labarai, matasa, wassani da al’adu na jiha kuma sabon kwamishinan aikin gona, Alhaji Alhassan Muhammad, ya sanar da haka yayin jawabi ga manema labarai bayan zaman majalisar.
Yace an amince da kashe kudi sama da Naira biliyan daya da miliyan dari domin samar da man dizel da sinadaran tsaftace ruwa da kuma gyaran injinan wuta, na tsawon shekara guda.
- Gwamnatin Sokoto Ta Bai Wa Sojojin Najeriya Gudummuwar Motocin Sulke 62
- Guguwar Iska Ta Kashe Mutane Uku, Ta Lalata Gidaje Da Ababen More Rayuwa A Yobe
- Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Takwas, Sun Kwato Makamai A Katsina
- Gwamnan Zamfara: Na Ƙi Biyan Kuɗin Fansa Naira Miliyan 300, Na Ce Su Kashe ‘Yan Uwana
- EFCC Ta Gurfanar da Bello Bodejo Kan Zargin Badaƙalar Kuɗi
Alhassan Muhammad yace majalisar ta kuma amince da kashe kudi sama da Naira miliyan dari da casa’in ta takwas domin cigaban aikin babban asibitin Gantsa ta karamar hukumar Buji, yayin da aka amince da kashe kudi Naira miliyan dari da casa’in da takwas domin makamancin wannan aikin a babban asibiti a Garki.