Majalisar zartarwar jihar Jigawa ta amince da bayar da kwangiloli wadanda kudinsu ya tasamma Naira biliyan daya da miliyan dari takwas a bangarorin ruwan sha da lafiya.
Tsohon kwamishinan yada labarai, matasa, wassani da al’adu na jiha kuma sabon kwamishinan aikin gona, Alhaji Alhassan Muhammad, ya sanar da haka yayin jawabi ga manema labarai bayan zaman majalisar.
Yace an amince da kashe kudi sama da Naira biliyan daya da miliyan dari domin samar da man dizel da sinadaran tsaftace ruwa da kuma gyaran injinan wuta, na tsawon shekara guda.
- Ana ci gaba da kaɗa ƙuri’a a zaben shugaban kasar Chadi
- An kashe ‘yan ta’adda da dama a hare-haren da jiragen yaki suka kai a Borno da Nijar
- Ministan Shari’a ya yi alkawarin sake duba dokar da ta haramta yunkurin kunar bakin wake a Najeriya
- Cibiyar ICAN ta karrama Gwamna Mallam Umar Namadi na Jihar Jigawa da lambar yabo
- Abba Kabir Yusuf ya musanta korar masu aikin tsaftace titi a jihar Kano
Alhassan Muhammad yace majalisar ta kuma amince da kashe kudi sama da Naira miliyan dari da casa’in ta takwas domin cigaban aikin babban asibitin Gantsa ta karamar hukumar Buji, yayin da aka amince da kashe kudi Naira miliyan dari da casa’in da takwas domin makamancin wannan aikin a babban asibiti a Garki.