Majalisar zartarwar jihar Jigawa ta amince da bayar da kwangiloli wadanda kudinsu ya tasamma Naira biliyan daya da miliyan dari takwas a bangarorin ruwan sha da lafiya.
Tsohon kwamishinan yada labarai, matasa, wassani da al’adu na jiha kuma sabon kwamishinan aikin gona, Alhaji Alhassan Muhammad, ya sanar da haka yayin jawabi ga manema labarai bayan zaman majalisar.
Yace an amince da kashe kudi sama da Naira biliyan daya da miliyan dari domin samar da man dizel da sinadaran tsaftace ruwa da kuma gyaran injinan wuta, na tsawon shekara guda.
- Airtel ta dakatar da bayar da bashin kati da data a Najeriya
- ’Yan adawa ba su isa su razanar da ni ba – Tinubu
- Sojoji sun kama masu satar man fetur a Legas, sun kama mutum 14
- Talauci ya ragu daga kaso 91 zuwa 41 a jihar Sokoto
- Bayan shekaru 12 da sace ɗaliban Chibok 272, har yanzu ba a san makomar 83 ba
Alhassan Muhammad yace majalisar ta kuma amince da kashe kudi sama da Naira miliyan dari da casa’in ta takwas domin cigaban aikin babban asibitin Gantsa ta karamar hukumar Buji, yayin da aka amince da kashe kudi Naira miliyan dari da casa’in da takwas domin makamancin wannan aikin a babban asibiti a Garki.