Kungiyar yan achaba ta jihar Kebbi ta nemi kariyar jami’an tsaro bayan barayi sun kashe yayan kungiyar hudu a jihar.
Shugaban kungiyar, Nafi’u Zaki, yayi kiran yayin wata ganawa da kamfanin dillancin labarai na kasa a Birnin Kebbi.
Nafi’u Zaki yace an kashe yayan kungiyar hudu a karamar hukumar Birnin Kebbi ta jihar.
- ‘Yan bindiga sun kashe babban limamin masallacin Juma’a na kauyen Keita
- Gobara ta ƙone motoci da rumfunan katako takwas da kuma kayan aikin kafinta ƙurmus
- Kwamitin Masallacin Dutse ya raba buhunan Shinkafa buhu 30,000 ga zawarawa da sauran marasa galihu
- Kwamandojin Boko Haram biyu sun mika wuya ga sojojin rundunar hadin gwiwa ta MNJTF
- Dan takarar jam’iyyar adawa Bassirou Diomaye Faye ne ke kan gaba a zaben shugaban kasar Senegal
Yace ana tsayar da mutanensu a dake su, wasu lokutan a yanke da wuka a kashe su.
Yace kafin yan kwanakinnan, kungiyar bata da rahoton wani dan kungiyar da aka kashe a kokarin kwace masa babur.
Nafi’u Zaki yace kungiyar tana da mambobi wadanda suka yi rijista su dubu talatin da bakwai, inda ya kara da cewa dayawa daga cikinsu sun fito daga kauyuka da jihoshi makota.