Wani mutum mai shekaru hamsin da daya a duniya wanda yansanda suka kira da mai yawan aikata fyade, an kama shi a jihar Katsina bisa zargin yiwa wasu yara su biyar fyade.
Mutumin mai suna Jabiru Audu, mazaunin unguwar Tundun Yanlahidda a Katsina, ana zargin ya yiwa yara mata biyar fyade, wadanda shekarunsu suka kama daga hudu zuwa goma sha biyu.
Yansanda sunce Jabiru Audu na zaune a gida daya da yaran tare da iyayensu.
- Airtel ta dakatar da bayar da bashin kati da data a Najeriya
- ’Yan adawa ba su isa su razanar da ni ba – Tinubu
- Sojoji sun kama masu satar man fetur a Legas, sun kama mutum 14
- Talauci ya ragu daga kaso 91 zuwa 41 a jihar Sokoto
- Bayan shekaru 12 da sace ɗaliban Chibok 272, har yanzu ba a san makomar 83 ba
Ana zargin yana aikata aika-aikar duk lokacin da kakar yaran wadanda suke zaune a wajenta, ta bar gida domin zuwa suyar kosai.
An gano cewa iyayen yaran ne suka kai rahoton lamarin ga babban ofishin yansanda na Katsina.
Kakakin rundunar yansandan jihar Katsina, SP Gambo Isah, ya tabbatar da lamarin ga manema labarai, inda ya kara da cewa Jabiru Audu ya amsa laifinsa.