

Gwamnan jihar Jigawa Muhammadu Badaru Abubakar ya amince da tura Alhaji Bala Ibrahim Mamsa a matsayin sabon kwamishina a ma’aikatar yada labarai, matasa, wassani da al’adu ta jiha.
Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa dauke da sa hannun sakataren gwamnatin jiha, Alhaji Adamu Abdulkadir Fanini, wacce aka rabawa manema labarai a Dutse.
- Why price of cement is high? -Dangote
- Tsohon Gwamnan Jihar Jigawa Ya Yiwa Gwamna Badaru Ta’aziyar Rasuwar Dan Uwansa
- Za A Yi Kididdigar Masu Aikin Karuwanci A Bauchi
- Kuji tsoron Allah ko koma gare Shi, Atiku yayi kira ga yan Najeriya.
- Goodluck Jonathan: Kuri’un talakawa ya kamata su tattance zabe ba kotu ba
Sanarwar tace gwamnan ya kuma amince da canja Alhaji Muhammad Alhassan daga ma’aikatar yada labarai, matasa, wassani da al’adu zuwa ma’aikatar aikin gona da ma’adanan kasa, a matsayin kwamishina.
Sanarwar ta yi kira ga kwamishinonin da su sadaukar da kawunansu wajen tabbatar da samun nasarar kudirori da tsare-tsaren gwamnatin Badaru, domin cigaban jihar baki daya.