Gwamnan jihar Jigawa Muhammadu Badaru Abubakar ya amince da tura Alhaji Bala Ibrahim Mamsa a matsayin sabon kwamishina a ma’aikatar yada labarai, matasa, wassani da al’adu ta jiha.
Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa dauke da sa hannun sakataren gwamnatin jiha, Alhaji Adamu Abdulkadir Fanini, wacce aka rabawa manema labarai a Dutse.
- Gwamnatin Sokoto Ta Bai Wa Sojojin Najeriya Gudummuwar Motocin Sulke 62
- Guguwar Iska Ta Kashe Mutane Uku, Ta Lalata Gidaje Da Ababen More Rayuwa A Yobe
- Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Takwas, Sun Kwato Makamai A Katsina
- Gwamnan Zamfara: Na Ƙi Biyan Kuɗin Fansa Naira Miliyan 300, Na Ce Su Kashe ‘Yan Uwana
- EFCC Ta Gurfanar da Bello Bodejo Kan Zargin Badaƙalar Kuɗi
Sanarwar tace gwamnan ya kuma amince da canja Alhaji Muhammad Alhassan daga ma’aikatar yada labarai, matasa, wassani da al’adu zuwa ma’aikatar aikin gona da ma’adanan kasa, a matsayin kwamishina.
Sanarwar ta yi kira ga kwamishinonin da su sadaukar da kawunansu wajen tabbatar da samun nasarar kudirori da tsare-tsaren gwamnatin Badaru, domin cigaban jihar baki daya.