Gwamnan jihar Jigawa Muhammadu Badaru Abubakar ya amince da tura Alhaji Bala Ibrahim Mamsa a matsayin sabon kwamishina a ma’aikatar yada labarai, matasa, wassani da al’adu ta jiha.
Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa dauke da sa hannun sakataren gwamnatin jiha, Alhaji Adamu Abdulkadir Fanini, wacce aka rabawa manema labarai a Dutse.
- Airtel ta dakatar da bayar da bashin kati da data a Najeriya
- ’Yan adawa ba su isa su razanar da ni ba – Tinubu
- Sojoji sun kama masu satar man fetur a Legas, sun kama mutum 14
- Talauci ya ragu daga kaso 91 zuwa 41 a jihar Sokoto
- Bayan shekaru 12 da sace ɗaliban Chibok 272, har yanzu ba a san makomar 83 ba
Sanarwar tace gwamnan ya kuma amince da canja Alhaji Muhammad Alhassan daga ma’aikatar yada labarai, matasa, wassani da al’adu zuwa ma’aikatar aikin gona da ma’adanan kasa, a matsayin kwamishina.
Sanarwar ta yi kira ga kwamishinonin da su sadaukar da kawunansu wajen tabbatar da samun nasarar kudirori da tsare-tsaren gwamnatin Badaru, domin cigaban jihar baki daya.