Muhimman Bayanan Da Ya Kamata Ku Sani Kan Mallam Ismaila Isa Funtua
Mutumin da ya samar da jaridar Democrat kuma tsohon shugaban kungiyar masu gidajen jarida na kasa, Mallam Ismaila Isa Funtua, ya rasu.
Ya mutu sanadiyyar bugun zuciya jiya Litinin da dare. Marigaryin ya rasu yana da shekaru saba’in da shida a duniya.
Babban mai taimakawa shugaban kasa akan kafafen yada labarai da hulda da jama’a, Mallam Garba Shehu, a cikin wata sanarwa yace shugaban kasa Muhammadu Buhari ya shiga matsananciyar damuwa da samun labarin mutuwar abokin tafiyarsa a siyasance, Isa Funtua.
- Amurka ta ce jami’anta na ganawa da sojojin da ke mulki a Jamhuriyar Nijar
- Gwamnatin jihar Jigawa ta fito da wani shiri na amfani da fasaha wajen koyo da koyarwa a jihar
- Kungiyar NULGE reshen karamar Hukumar Buji ta yabawa wakilin mazabar Buji a majalisar dokoki
- Aƙalla fursunoni 118 ne suka tsere daga gidan yarin Suleja
- Kasashen Afirka sun amince su yi magana da murya daya domin yaki da ta’addanci
Ana kyautata zaton cewa Isa Funtua na daya daga cikin masu karfin fada aji a gwamnatin Buhari.
Ance Isa Funtua tare da tsohon shugaban ma’aikatan shugaban kasa Abba Kyari da dan yayan shugaban kasa, Mamma Daura, sune wadanda suka fi kowa karfin iko a gwamnatin Buhari.