Mutumin da ya samar da jaridar Democrat kuma tsohon shugaban kungiyar masu gidajen jarida na kasa, Mallam Ismaila Isa Funtua, ya rasu.
Ya mutu sanadiyyar bugun zuciya jiya Litinin da dare. Marigaryin ya rasu yana da shekaru saba’in da shida a duniya.
Babban mai taimakawa shugaban kasa akan kafafen yada labarai da hulda da jama’a, Mallam Garba Shehu, a cikin wata sanarwa yace shugaban kasa Muhammadu Buhari ya shiga matsananciyar damuwa da samun labarin mutuwar abokin tafiyarsa a siyasance, Isa Funtua.
- Ronaldo ya yi alfahari da ɗansa ya buga wa Portugal tamaula
- Gwamna Uba Sani Ya Kafa Sabon Tarihi, Ya Yi Abin da ba a Taba Yi ba a Najeriya
- Tsohun gwamnan jihar Benue,ya baiyana cewa jam’iyyar PDP tana cikin mawuyacin hali da zai iya kai ta ga rushewa kafin 2027
- Sojoji masu mulkin Mali sun rusa dukkan jam’iyyun siyasa a kasar
- NiMET, ta fitar da sabon hasashen yanayi inda tace da yiwuwar ɓarkewar cututtukan ruwa a karshe shekara 2025
Ana kyautata zaton cewa Isa Funtua na daya daga cikin masu karfin fada aji a gwamnatin Buhari.
Ance Isa Funtua tare da tsohon shugaban ma’aikatan shugaban kasa Abba Kyari da dan yayan shugaban kasa, Mamma Daura, sune wadanda suka fi kowa karfin iko a gwamnatin Buhari.