Muhimman Bayanan Da Ya Kamata Ku Sani Kan Mallam Ismaila Isa Funtua

0 114

Mutumin da ya samar da jaridar Democrat kuma tsohon shugaban kungiyar masu gidajen jarida na kasa, Mallam Ismaila Isa Funtua, ya rasu.

Ya mutu sanadiyyar bugun zuciya jiya Litinin da dare. Marigaryin ya rasu yana da shekaru saba’in da shida a duniya.

Babban mai taimakawa shugaban kasa akan kafafen yada labarai da hulda da jama’a, Mallam Garba Shehu, a cikin wata sanarwa yace shugaban kasa Muhammadu Buhari ya shiga matsananciyar damuwa da samun labarin mutuwar abokin tafiyarsa a siyasance, Isa Funtua.

Ana kyautata zaton cewa Isa Funtua na daya daga cikin masu karfin fada aji a gwamnatin Buhari.

Ance Isa Funtua tare da tsohon shugaban ma’aikatan shugaban kasa Abba Kyari da dan yayan shugaban kasa, Mamma Daura, sune wadanda suka fi kowa karfin iko a gwamnatin Buhari.

Leave a Reply

%d bloggers like this: