Bola Ahmed Tinubu ya ce Allah na iya bayar da mulki ga duk wanda yaga dama

Jagoran Jam’iyyar APC na Kasa, Bola Ahmed Tinubu, ya ce Allah na iya bayar da mulki ga duk wanda yaga dama.

Bola Tinubu ya fadi haka ne jiya a Legas yayin da ya sake haduwa da abokan siyasarsa da masu kare shi a wani taron maraba da addu’o’i, wanda Gwamna Babajide Sanwo-Olu ya shirya.

Taron shine farkon fitowar Tinubu tun bayan dawowarsa daga Burtaniya a daren Juma’a, bayan watanni uku ba ya kasar.

Jagoran Jam’iyyar APC na kasa, wanda rahotanni ke cewa yana sha’awar neman kujerar shugaban kasa a shekarar 2023, ya ce abin da Allah ke bukata daga duk wanda Ya ba shi mulki shi ne ya amfanar da mutane.

Ya ce taron addu’ar ya kasance mai soyuwa a gare shi, yayin da fatan alheri daga ‘yan Najeriya da suka yi masa fatan alkhairi yayin da ba ya nan.

Gwamna Sanwo-Olu ya ce dawowar Tinubu labarine mai faranta rai ga magoya bayansa a duk fadin kasarnan.

Comments (0)
Add Comment