Buhari Ya Amince A Fara Biyan Sabbin Ma’aikata 774,000 Albashi

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya amince a fitar da kudade domin a fara biyan albashin ma’aikata 774,000 da aka dauka domin gudanar da wasu ayyuka na musamman a yankunansu.

Minista a Ma’aikatar Kwadago da Samar da Ayyukan yi, Festus Keyamo ne ya sanar da hakan a wani sako da ya wallafa a shafinsa na Twitter ranar Asabar.

Ministan ya kuma ce tuni ya umarci Hukumar Samar da Ayyuka ta Kasa (NDE) da ta shirya biyan kudaden ma’aikatan a Kananan Hukumomi 774 na Najeriya.

A watan Janairun wannan shekar nan ne dai Gwamnatin Tarayya ta kaddamar da shirin wanda zai samarwa da matasa 1,000 da ayyukan yi daga dukkan Kananan Hukumomin Najeriya 774.

A cikin shirin dai, an tsara za a rika biyan kowannensu N20,000 har na tsawon watanni uku masu zuwa.

Minista Keyamo ya ce za a rika biyan matasan ne ta asusun ajiyarsu na bankuna da suka bayar yayin rijista.

Sai dai ya ce za a yi amfani ne da Lambar Tantancewarsu ta Banki ta BVN domin kaucewa almundahana a yayin biyan.

Sai dai ya ce dukkan wadanda suka yi rijista da wasu sunayen na daban ba za su sami ko sisin kwabo ba.

BuhariDAUKAR AIKIMaaikataSHUGABA BUHARI
Comments (0)
Add Comment