Rundunar yansandan jihar kano tace, kawo yanzu ta tantance masu neman shiga aikin kurtun dan sanda dubu 13 da 40 kwanaki 11 bayan tafara aikin tantancewar a jihar kano.
Mai magana da yawun rundunar yansandan jihar ta kano DSP Abdullahi Haruna,shine ya bayyana hakan yayin gudaanar da aikin tantancewar a jiya juma,a a birnin kano.
DSP Haruna,ya kara da cewa wadanda aka tantance din sun fito ne daga kananan hukumomi 40 daga cikin 44 dake fadin jihar ta kano.
A cewar DSP Abdullahi Haruna, mutune 1,475 sunfito ne daga kananan hukumomin Takai, Tarauni, Tofa and Tsanywa wadanda aka tantance su a ranar alhamis din data gabata.
Sannna ya kara da cewa a ranar jum,aa,a mai zuwa zasu kammala gudanar aikin tantancewar a fadin jhar ta kano.
A cewar sa mutanen da suka rasa shiga aikin aikin tantancewar a kananan hukumomin Tudun Wada, Warawa, Wudil and Ungogo, nan gaba bada dadewa ba, za,a sanar da su ranar da zasu zo domin a tantance su.
- Ana ci gaba da kaɗa ƙuri’a a zaben shugaban kasar Chadi
- An kashe ‘yan ta’adda da dama a hare-haren da jiragen yaki suka kai a Borno da Nijar
- Ministan Shari’a ya yi alkawarin sake duba dokar da ta haramta yunkurin kunar bakin wake a Najeriya
- Cibiyar ICAN ta karrama Gwamna Mallam Umar Namadi na Jihar Jigawa da lambar yabo
- Abba Kabir Yusuf ya musanta korar masu aikin tsaftace titi a jihar Kano
Sannan ya kara da cewa suna gudanar da aikin tantancewar ne cikin matakan kariya daga cutar corona kamar yanda aka umarce su.