Rundunar yansandan jihar kano tace, kawo yanzu ta tantance masu neman shiga aikin kurtun dan sanda dubu 13 da 40 kwanaki 11 bayan tafara aikin tantancewar a jihar kano.
Mai magana da yawun rundunar yansandan jihar ta kano DSP Abdullahi Haruna,shine ya bayyana hakan yayin gudaanar da aikin tantancewar a jiya juma,a a birnin kano.
DSP Haruna,ya kara da cewa wadanda aka tantance din sun fito ne daga kananan hukumomi 40 daga cikin 44 dake fadin jihar ta kano.
A cewar DSP Abdullahi Haruna, mutune 1,475 sunfito ne daga kananan hukumomin Takai, Tarauni, Tofa and Tsanywa wadanda aka tantance su a ranar alhamis din data gabata.

Sannna ya kara da cewa a ranar jum,aa,a mai zuwa zasu kammala gudanar aikin tantancewar a fadin jhar ta kano.
A cewar sa mutanen da suka rasa shiga aikin aikin tantancewar a kananan hukumomin Tudun Wada, Warawa, Wudil and Ungogo, nan gaba bada dadewa ba, za,a sanar da su ranar da zasu zo domin a tantance su.
- Barcelona ta ba Lamine Yamal lamba 10
- An ɗaura auren Umaru Musa Yar’Adua Jnr., ɗan marigayi tsohon shugaban ƙasa, Alhaji Umaru Musa Yar’Adua, tare da amaryarsa Maryam Ayuba Shuaibu
- Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Alhaji Atiku Abubakar (GCON), ya kawo karshen shakku da tsokaci, inda a hukumance ya fice dga jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP),
- Manhajar TikTok ta goge fiye da bidiyo miliyan 3.6 a Najeriya saboda saba ka’idar dokokinta
- Tsohon Shugaban APC na ƙasa kuma tsohon Gwamnan Jihar Edo, ya fice daga jam’iyya APC zuwa jam’iyyar hadaka ta ADC
Sannan ya kara da cewa suna gudanar da aikin tantancewar ne cikin matakan kariya daga cutar corona kamar yanda aka umarce su.