Ofishin hukumar wayar da kan jama`a ta kasa a jihar Jigawa ta gudanar da taron gangami a karamar hukumar Malam-Madori domin fadakar da al`umma illolin da cutar Korona virus ta haifar a fannonin tsaro da zamantakewa.
A jawabin da ya gabatar Daraktan hukumar na jiha, Malam Shu`aibu Karamba Haruna yayi dogon bayani akan matakan da ya kamata a dauka domin kare yaduwar cutar Covid-19.
- Amurka ta ce jami’anta na ganawa da sojojin da ke mulki a Jamhuriyar Nijar
- Gwamnatin jihar Jigawa ta fito da wani shiri na amfani da fasaha wajen koyo da koyarwa a jihar
- Kungiyar NULGE reshen karamar Hukumar Buji ta yabawa wakilin mazabar Buji a majalisar dokoki
- Aƙalla fursunoni 118 ne suka tsere daga gidan yarin Suleja
- Kasashen Afirka sun amince su yi magana da murya daya domin yaki da ta’addanci
Haka kuma ya bukaci jama`a su tabbatar suna bin dukkanin ka`idojin da hukumomin lafiya suka tanada domin kare yaduwar cutar.
A lokacin gangamin wani jami`in hukumar wayar da kan jama`a ta kasa, Malam Tijjani ya gabatar da makala mai taken tasirin cutar Covid-19 akan tattalin arziki da karuwar aikata laifuka da kuma rigingimu tsakanin Fulani da manoma.
A nasa jawabin shugaban karamar hukumar Malam-Madori wanda ya sami wakilcin Daraktan tsare-tsare na yankin, Malam Lawan Bawa ya jaddada kudurin karamar hukumar na hada kai da hukumar domin cimma biyan bukata.
Mahalarta taron sun hadar da yan`kungiyoyi masu zaman kansu da kungiyar Miyetti Allah da jami`an hukumar kiyaye haddura ta kada limamai da masu ruwa da tsaki.