

- Anyi hasashen samun ruwan sama hade da tsawa a fadin kasarnan daga yau zuwa ranar Laraba - August 23, 2021
- Wata kungiyar adawa ta ce tana da dubban mayaka da zasu fafata yaki da yan Taliban a Afghanistan - August 23, 2021
- ‘Yan bindiga sun kashe mutane 4 tare da sace wasu 50 a karamar hukumar Maradun ta jihar Zamfara - August 23, 2021
Kimanin mutane 23 ne suka rasa rayukansu a sakamakon illar da ambaliyar ruwa ta haifar a jihar Jigawa wanda yayi sanadiyyar raba mutane dubu 51 da muhallinsu a kananan hukumomi sama da 24 a nan jihar.
Babban sakataren hukumar bada agajin gaggawa ta jihar Jigawa SEMA Yusuf Babura shine ya tabbatar da mutuwar mutane 21 a jiya, wanda yace mafiya yawa kananan yara ne.
Babura yace dayawa daga cikin wanda ambaliyar ruwan ta shafa sun rasa rayukansu a sakamakon rushewar gini wanda mamakon ruwan sama ya haifar a yankunan, sai sauran da igiyar ruwa ta hallaka.
Haka kuma yace sama da iyalai dubu 50 sun kauracewa muhallinsu na gado, a yayinda akayi asarar dubban kadadan filayen noma tare da tare da rasa kayan amfanin noma.
Yankunan da lamarin ya shafa sun hada da kauyukan Maruta, Babaldu, Samamiya duka a kananan hukumomin Birnin Kudu da Gwaram. Kayan amfanin gonar da akayi asara kuwa suna kamar haka Yabanyar Dawa, Masara, Shinkafa, da Gero, wanda kudin yakai kimanin biliyoyin Nairori.
- Yadda yan IPOB suka kashe ‘yan Arewa 10 ciki har da mace mai juna biyu da ‘ya’yanta 4 da wasu mutane 6 a jihar Anambra
- Sama da mutane 30 ne aka ruwaito sun bace a jihar Borno bayan da wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kai musu hari
- Tsohon gwamnan jihar Gombe, Ibrahim Dankwambo, ya karbi tikitin takarar Sanatan Gombe ta Arewa domin tsayawa takara a jam’iyyar PDP a 2023
- Yadda Ibrahim Saminu Turaki ya kasance dan takarar sanata mai wakiltar mazabar Jigawa ta Arewa maso Yamma – PDP
- Ma’aikatar kula da muhalli ta jihar Jigawa ta yi barazanar daukar mataki akan wanda aka samu da laifin cin iyakar makiyaya
Kazalika aftilain ya shafi kananan kukumomi 24 daga cikin kananan kumomi 27 na jihar, wanda kuma abin yafi Kamari a kananan hukumomi 17. Babura yace kawo yanzu, hukumar bada agajin ta dunguma shirin raba kayan tallafi ga alumar da iftilain ya shafa, wanda dayawa daga cikin su suka yi hijira zuwa makarantu da zama