Kungiyoyi 80 zasu yi zanga-zanga a Nijeriya har da ta kwadago

0 97

Gamayyar kungiyyar yan kasuwa da wasu kungiyoyiyn farar hula 79 da kuma kungiyyar yan kwadago sun kudiri anniyar gudanar da wata zanga zangar limana a fadin kasar nan a sati mai zuwa saboda karin kudin man fetir da na wutar lantarki da kayi a fadin kasar nan.

An rawaito cewa kungiyyar yan kwadago a jiya ta gudanar da wani taron tattaunawa domin samun bakin zaren yanda zasu gudanar da zanga zangar

A lokacin da ya ke tabbatar da zanga zangar ta wayar tarho a jiya juma,a , babban lauyan nan mai rajin kar hakkin bil,adama na kasa Mr Femi Falana yace karin kudin mai da na wutar lantarkin da kuma na kayan masarufi da gwamanti tayi shaidanci ne.

A cewar sa wasu kasashe na duniya na saukakawa yan kasar ta kudaden haraji dana sauran abubuwan amfanin yau da kullum amma gwamnatin kasar na yin akasin haka.

Leave a Reply

%d bloggers like this: