Nigeria zata buga wasannin sada zumunci a Austria

0 104

Ƙungiyar ƙwallon ƙafar Nigeria Super Eagles zata yi wassannin sada zumunci 2 a watan October. Shugaban ƙwallon ƙafar Nigeria Amaju Pinnick ne ya sanar da hakan a shafinsa na twitter.

Pinnick yace “Super Eagle zata yi wasan sada zumuncin ne ranar 9 ga watan october da Cote D’lvioier, kana daga bisani ta sake wata karawar da Tunisia ranar 13 ga wata.”

Yace duk wasanin za’ayi sune a ƙasar Austria sabida wasu ƴan dalilai.

Sabida dokoki na COVID-19 aka zabi Austria gurin da za’a gudanar da wasanin.

Leave a Reply

%d bloggers like this: