Kwamitin duban wata na kasa a karkashin majalisar koli ta harkokin addinin Islama a Najeriya yace ba a samu rahoton ganin sabon watan Muharram ba, na shekarar 1442 bayan hijrah.
Hakan na nufin cewa yau, Alhamis ita ce ranar talatin ga watan Dhul-Hijjah, shekara ta 1442 bayan hijrah, yayin da gobe Juma’a zata zamo daya ga watan Muharamm, a sabuwar shekarar musulunci ta 1442 bayan hijrah.
- Sarki Charles zai koma aiki makon gobe
- Amurka ta bayar da bayanin tallafin soji na $6Bn da ta bai wa Ukriane
- Japan za ta taimakawa ƙananan ma’aikata a Najeriya domin samar da shinkafa
- Gwamnatin Jigawa ta jadadda kudirinta na daukar kwararan matakai na rage talauci a jihar
- An kama haramtattun nakiyoyi 6,240 a hanyar Yauri zuwa Jega da ke Jihar Kebbi
Wani mamba a kwamitin na duban watan na kasa, Sheikh Salihu Muhammad Yakubu, ya shaidawa manema labarai hakan, jiya da dare.
An bayar da rahoton cewa Farfesa Sambo Wali Junaidu, Wazirin Sokoto, kuma shugaban kwamitin shura kan harkokin addini a majalisar mai alfarma sarkin musulmi a Sokoto, cikin wata sanarwa a ranar Litinin, yace jiya Laraba ce ranar da za a fara duban sabon watan Muharram, shekara ta 1442 Bayan Hijrah.