Kwamitin duban wata na kasa a karkashin majalisar koli ta harkokin addinin Islama a Najeriya yace ba a samu rahoton ganin sabon watan Muharram ba, na shekarar 1442 bayan hijrah.
Hakan na nufin cewa yau, Alhamis ita ce ranar talatin ga watan Dhul-Hijjah, shekara ta 1442 bayan hijrah, yayin da gobe Juma’a zata zamo daya ga watan Muharamm, a sabuwar shekarar musulunci ta 1442 bayan hijrah.
- ‘Yan bindiga sun kashe babban limamin masallacin Juma’a na kauyen Keita
- Gobara ta ƙone motoci da rumfunan katako takwas da kuma kayan aikin kafinta ƙurmus
- Kwamitin Masallacin Dutse ya raba buhunan Shinkafa buhu 30,000 ga zawarawa da sauran marasa galihu
- Kwamandojin Boko Haram biyu sun mika wuya ga sojojin rundunar hadin gwiwa ta MNJTF
- Dan takarar jam’iyyar adawa Bassirou Diomaye Faye ne ke kan gaba a zaben shugaban kasar Senegal
Wani mamba a kwamitin na duban watan na kasa, Sheikh Salihu Muhammad Yakubu, ya shaidawa manema labarai hakan, jiya da dare.
An bayar da rahoton cewa Farfesa Sambo Wali Junaidu, Wazirin Sokoto, kuma shugaban kwamitin shura kan harkokin addini a majalisar mai alfarma sarkin musulmi a Sokoto, cikin wata sanarwa a ranar Litinin, yace jiya Laraba ce ranar da za a fara duban sabon watan Muharram, shekara ta 1442 Bayan Hijrah.