Shugaban hukumar shige da fice ta kasa Muhammad Babandede yayi zargin cewa akwai almundahana a wata kwangilar katin shaidar zama a kasa domin kwararru ‘yan kasashen waje, wacce aka sanyawa hannu tsakanin ma’aikatar cikin gida da wani kamfanin fasaha a shekarar 2007.
Kamfanin abokin hulda ne na hukumar shige da fice ta kasa, wajen samar da katin shaidar zama a kasa domin kwararru ‘yan kasashen waje.
- ‘Yan bindiga sun kashe babban limamin masallacin Juma’a na kauyen Keita
- Gobara ta ƙone motoci da rumfunan katako takwas da kuma kayan aikin kafinta ƙurmus
- Kwamitin Masallacin Dutse ya raba buhunan Shinkafa buhu 30,000 ga zawarawa da sauran marasa galihu
- Kwamandojin Boko Haram biyu sun mika wuya ga sojojin rundunar hadin gwiwa ta MNJTF
- Dan takarar jam’iyyar adawa Bassirou Diomaye Faye ne ke kan gaba a zaben shugaban kasar Senegal
Katin shaidar tilas ne ga kwararru ‘yan kasashen waje a Najeriya. Yana basu daman su zauna tare da yin aiki a kasarnan, kuma ana iya sabunta shi kowace shekara, ko bayan shekara biyu, dogaro da shekarun aikin da aka sanya masa.
Zarge-zargen sun zo kimanin watanni goma sha takwas bayan ma’aikatar cikin gida, karkashin tsohon minista Abdurrahman Dambazau, ta kara farashin katin daga Dala dubu daya zuwa Dala dubu biyu a ranar goma sha uku ga watan Disambar 2018, biyo bayan bukatar hakan da kamfanin ya nema.