

Shugaban hukumar shige da fice ta kasa Muhammad Babandede yayi zargin cewa akwai almundahana a wata kwangilar katin shaidar zama a kasa domin kwararru ‘yan kasashen waje, wacce aka sanyawa hannu tsakanin ma’aikatar cikin gida da wani kamfanin fasaha a shekarar 2007.
Kamfanin abokin hulda ne na hukumar shige da fice ta kasa, wajen samar da katin shaidar zama a kasa domin kwararru ‘yan kasashen waje.
- Abubuwa 5 da suka zama wajibi lokacin sanyi
- An ƙaddamar da kudin kariya ga ƴan jarida da masu fafutukar ƴancin amfani da yanar gizo
- Yadda ake duba suna don zama ma’aikacin damara na 2020 a Nijeria
- Me Ƙungiyar Izala ta ce kan matsalolin tsaro a Najeriya?
- Muhimmiyar shawara ga manoma kan Noman rani
Katin shaidar tilas ne ga kwararru ‘yan kasashen waje a Najeriya. Yana basu daman su zauna tare da yin aiki a kasarnan, kuma ana iya sabunta shi kowace shekara, ko bayan shekara biyu, dogaro da shekarun aikin da aka sanya masa.

Zarge-zargen sun zo kimanin watanni goma sha takwas bayan ma’aikatar cikin gida, karkashin tsohon minista Abdurrahman Dambazau, ta kara farashin katin daga Dala dubu daya zuwa Dala dubu biyu a ranar goma sha uku ga watan Disambar 2018, biyo bayan bukatar hakan da kamfanin ya nema.