

Kwamishinan kasuwanci da masana’antu na jihar Bauchi, Mohammed Sadiq, yayi murabus daga mukaminsa.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na Facebook.
Kwamishinan a sanarwar tasa, ya godewa tsohon kakakin majalisar wakilai ta kasa, Yakubu Dogara, wanda a cewarsa shine yayi silar bashi mukamin.
- Tarihin Gamuwa 10 Tsakanin Kano Pillars VS Eyimba Da Kuma Wasan Yau
- Abubuwa 5 da suka zama wajibi lokacin sanyi
- An ƙaddamar da kudin kariya ga ƴan jarida da masu fafutukar ƴancin amfani da yanar gizo
- Yadda ake duba suna don zama ma’aikacin damara na 2020 a Nijeria
- Me Ƙungiyar Izala ta ce kan matsalolin tsaro a Najeriya?
Hadimin Yakubu Dogara mai yada labarai, Turaki Hassan, shima ya yada sanarwar ta sa.
Wata daya baya, Yakubu Dogara, ya fice daga jam’iyyar PDP, inda ya koma tsohuwar jam’iyyarsa ta APC.
Ficewar tasa daga jam’iyyar tazo ne bayan rikici tsakaninsa da gwamnan jihar, Bala Mohammed.