Kwamishinan kasuwanci da masana’antu na jihar Bauchi, Mohammed Sadiq, yayi murabus daga mukaminsa.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na Facebook.
Kwamishinan a sanarwar tasa, ya godewa tsohon kakakin majalisar wakilai ta kasa, Yakubu Dogara, wanda a cewarsa shine yayi silar bashi mukamin.
- Gwamnatin Sokoto Ta Bai Wa Sojojin Najeriya Gudummuwar Motocin Sulke 62
- Guguwar Iska Ta Kashe Mutane Uku, Ta Lalata Gidaje Da Ababen More Rayuwa A Yobe
- Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Takwas, Sun Kwato Makamai A Katsina
- Gwamnan Zamfara: Na Ƙi Biyan Kuɗin Fansa Naira Miliyan 300, Na Ce Su Kashe ‘Yan Uwana
- EFCC Ta Gurfanar da Bello Bodejo Kan Zargin Badaƙalar Kuɗi
Hadimin Yakubu Dogara mai yada labarai, Turaki Hassan, shima ya yada sanarwar ta sa.
Wata daya baya, Yakubu Dogara, ya fice daga jam’iyyar PDP, inda ya koma tsohuwar jam’iyyarsa ta APC.
Ficewar tasa daga jam’iyyar tazo ne bayan rikici tsakaninsa da gwamnan jihar, Bala Mohammed.