Hukumar bada agajin gaggawa ta kasa tayi hasashen samun ambaliyar ruwa a kananan hukumomi 12 na jihar Jigawa.
Jami’in hukumar mai kula da ofishin hukumar na shiyyar Kano, Sanusi Ado ya bayyana haka a lokacin gangamin wayar da kan alumma kan matakan kariya daga ambaliyar ruwa a Dutse.
Jami’in wanda ya samu wakilcin mataimakin darakta a hukumar, Aminu Boyi Ringim, yace kananan hukumomin da ake hasashen samun ambaliyar ruwan sune Ringim da Kaugama da Taura da Guri da Gwaram da Dutse da Auyo da Miga da Malam-Madori da Birniwa da Jahun da kuma Kafin Hausa.
- Gwamnatin Jigawa ta jadadda kudirinta na daukar kwararan matakai na rage talauci a jihar
- An kama haramtattun nakiyoyi 6,240 a hanyar Yauri zuwa Jega da ke Jihar Kebbi
- Gwamnati na shirin farfado da masaku da nufin bunkasa noman auduga da samar da tufafi
- Hukumomi na aiki da jami’an tsaro wajen kamo duka ragowar fursunoni 109 da suka tsere daga gidan gyaran hali
- Za’a gudanar da cikakken bincike don tabbatar da ingancin duka jiragen sama da ke zirga-zirga a Najeriya
Sanusi Ado ya kara da cewa sun ziyarci jihar Jigawa ne domin wayar da kan alumma kan matakan kare kai daga ambaliyar ruwan da ake hasashen samu a bana.
Tun da farko a jawabinsa sakataren zartarwa na hukumar bada agajin gaggawa ta jiha, Yusif Sani Babura, ya godewa hukumar bisa zabar jihar Jigawa domin gudanar da gangamin wayar da kan.