Hukumar bada agajin gaggawa ta kasa tayi hasashen samun ambaliyar ruwa a kananan hukumomi 12 na jihar Jigawa.
Jami’in hukumar mai kula da ofishin hukumar na shiyyar Kano, Sanusi Ado ya bayyana haka a lokacin gangamin wayar da kan alumma kan matakan kariya daga ambaliyar ruwa a Dutse.
Jami’in wanda ya samu wakilcin mataimakin darakta a hukumar, Aminu Boyi Ringim, yace kananan hukumomin da ake hasashen samun ambaliyar ruwan sune Ringim da Kaugama da Taura da Guri da Gwaram da Dutse da Auyo da Miga da Malam-Madori da Birniwa da Jahun da kuma Kafin Hausa.
- Ina alfahari da samun dimbin goyon bayan da ake bukata domin zama ‘yartakara – Kamala Harris
- An bukaci mazauna jihar Jigawa da su kula da matakan kariya domin dakile ambaliyar ruwa
- Ƙasashe 58 sun goyi bayan Ngozi Okonjo-Iweala ta yi tazarce a Shugabar Kungiyar Cinikayya ta Duniya
- Kungiyar Kwadago ta yi gargadi kan yunkurin dakushe zanga-zangar da ake shirin yi a fadin kasar
- Gwamnatin Tarayya ta gabatar da buƙatar ƙarin Naira tiriliyan 6.2 akan kasafin kuɗin bana
Sanusi Ado ya kara da cewa sun ziyarci jihar Jigawa ne domin wayar da kan alumma kan matakan kare kai daga ambaliyar ruwan da ake hasashen samu a bana.
Tun da farko a jawabinsa sakataren zartarwa na hukumar bada agajin gaggawa ta jiha, Yusif Sani Babura, ya godewa hukumar bisa zabar jihar Jigawa domin gudanar da gangamin wayar da kan.