Shugaban majalissar Dattawa ta kasa Femi Gbajabiamila, yace Gwamnan Jihar Lagas Babajide Sanwo-Olu yace jihar tana bukatar Naira Tiriliyan Daya domin a sake gina wajen da masu zanga-zangar #EndSARs suka rushe.
Gbajabiamila ya fadi haka a lokacin da yake hira da yan jaridu a majalissar bayan ziyarar gani da ido kan wuraren da masu zanga zangar suka barnatar a birnin Lagas.
- Gwamnatin Jigawa zata cigaba da tallafawa Jami’ar Fasaha ta gwamnatin tarayya dake garin Babura
- Aƙalla mutum 42 ne suka mutu sakamakon ƙyanda a jihar Adamawa
- Gwamnan Jihar Gombe ya yi kira ga sabbin zababbun shugabannin kananan hukumomi da su yi aiki tukuru
- Gwamna Dikko Radda ya kare ziyarar da gwamnonin Arewa suka kai kasar Amurka
- Kasar Turkiyya ta dakatar da duk wata hulɗar kasuwanci da Isra’ila
Ya ce majalissar zatayi duk mai yuwuwa domin biyan diyya ga wadanda rikicin ya rutsa da su, da suka hadar da jami’an yan sanda da suka rasa rayukansu.
Ya kuma bukaci matasa da kwantar da hankulansu, domin dawo da zaman lafiya, tare da bayyana kwarin gwiwarsa kan hadin kan kasa.