Shugaban majalissar Dattawa ta kasa Femi Gbajabiamila, yace Gwamnan Jihar Lagas Babajide Sanwo-Olu yace jihar tana bukatar Naira Tiriliyan Daya domin a sake gina wajen da masu zanga-zangar #EndSARs suka rushe.
Gbajabiamila ya fadi haka a lokacin da yake hira da yan jaridu a majalissar bayan ziyarar gani da ido kan wuraren da masu zanga zangar suka barnatar a birnin Lagas.
- Gwamnatin Gombe Ta Ware N260m Don Sauya Wa Kasuwar Hatsi Matsuguni
- TUC Za Ta Karfafa Haɗin Gwiwa da Gwamnatin Jigawa Don Walwalar Ma’aikata
- Mutum 3,000 Sun Yi Hijira Saboda Hare-Haren ’Yan Bindiga A Katsina
- An Kama Jami’in DSS Na Bogi A Abuja
- Davido Aka So Kashewa A Harin da Aka Kai Wa Tawagar Adeleke — ’Yan Sanda
Ya ce majalissar zatayi duk mai yuwuwa domin biyan diyya ga wadanda rikicin ya rutsa da su, da suka hadar da jami’an yan sanda da suka rasa rayukansu.
Ya kuma bukaci matasa da kwantar da hankulansu, domin dawo da zaman lafiya, tare da bayyana kwarin gwiwarsa kan hadin kan kasa.