Hukumar Shari’a ta Jihar Jigawa, ta dakatar da dogon hutun da Alkalai suke zuwa duk shekara, wanda kuma zasu fara tafiya hutun daga 13 ga watan Yuli na shekarar da muke ciki.
Wannan yana cikin Doka Mai Namba 5 na shekarar 2020 da Babban Alkalin Jiha, kuma shugaban Majalisar Hukumar Shari’a Hon Aminu Sabo Ringim, ya sanyawa hannun.
- Gwamnatin Sokoto Ta Bai Wa Sojojin Najeriya Gudummuwar Motocin Sulke 62
- Guguwar Iska Ta Kashe Mutane Uku, Ta Lalata Gidaje Da Ababen More Rayuwa A Yobe
- Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Takwas, Sun Kwato Makamai A Katsina
- Gwamnan Zamfara: Na Ƙi Biyan Kuɗin Fansa Naira Miliyan 300, Na Ce Su Kashe ‘Yan Uwana
- EFCC Ta Gurfanar da Bello Bodejo Kan Zargin Badaƙalar Kuɗi
A cewarsa, matakin ya biyo bayan yadda aka kwashe lokaci mai tsayi Alkalan suna zaman gida, saboda cutar Corona.
Haka kuma ya ce saboda yadda ake da Shari’oi da yawa da suke jiran a yanke musu hukunci, ya zama dole a dakatar da wannan Hutun saboda a samu rage Cunkoso a gidajen Yari.
Kazalika, ya ce Dakatar da Dokar, yana cikin kundin tsarin Mulkin Kasa na shekarar 1999, wanda aka yi masa Kwaskwarima.