Hukumar Shari’a ta Jihar Jigawa, ta dakatar da dogon hutun da Alkalai suke zuwa duk shekara, wanda kuma zasu fara tafiya hutun daga 13 ga watan Yuli na shekarar da muke ciki.
Wannan yana cikin Doka Mai Namba 5 na shekarar 2020 da Babban Alkalin Jiha, kuma shugaban Majalisar Hukumar Shari’a Hon Aminu Sabo Ringim, ya sanyawa hannun.
- Ronaldo ya yi alfahari da ɗansa ya buga wa Portugal tamaula
- Gwamna Uba Sani Ya Kafa Sabon Tarihi, Ya Yi Abin da ba a Taba Yi ba a Najeriya
- Tsohun gwamnan jihar Benue,ya baiyana cewa jam’iyyar PDP tana cikin mawuyacin hali da zai iya kai ta ga rushewa kafin 2027
- Sojoji masu mulkin Mali sun rusa dukkan jam’iyyun siyasa a kasar
- NiMET, ta fitar da sabon hasashen yanayi inda tace da yiwuwar ɓarkewar cututtukan ruwa a karshe shekara 2025
A cewarsa, matakin ya biyo bayan yadda aka kwashe lokaci mai tsayi Alkalan suna zaman gida, saboda cutar Corona.
Haka kuma ya ce saboda yadda ake da Shari’oi da yawa da suke jiran a yanke musu hukunci, ya zama dole a dakatar da wannan Hutun saboda a samu rage Cunkoso a gidajen Yari.
Kazalika, ya ce Dakatar da Dokar, yana cikin kundin tsarin Mulkin Kasa na shekarar 1999, wanda aka yi masa Kwaskwarima.