

Hukumar Shari’a ta Jihar Jigawa, ta dakatar da dogon hutun da Alkalai suke zuwa duk shekara, wanda kuma zasu fara tafiya hutun daga 13 ga watan Yuli na shekarar da muke ciki.
Wannan yana cikin Doka Mai Namba 5 na shekarar 2020 da Babban Alkalin Jiha, kuma shugaban Majalisar Hukumar Shari’a Hon Aminu Sabo Ringim, ya sanyawa hannun.
- Abubuwa 5 da suka zama wajibi lokacin sanyi
- An ƙaddamar da kudin kariya ga ƴan jarida da masu fafutukar ƴancin amfani da yanar gizo
- Yadda ake duba suna don zama ma’aikacin damara na 2020 a Nijeria
- Me Ƙungiyar Izala ta ce kan matsalolin tsaro a Najeriya?
- Muhimmiyar shawara ga manoma kan Noman rani
A cewarsa, matakin ya biyo bayan yadda aka kwashe lokaci mai tsayi Alkalan suna zaman gida, saboda cutar Corona.
Haka kuma ya ce saboda yadda ake da Shari’oi da yawa da suke jiran a yanke musu hukunci, ya zama dole a dakatar da wannan Hutun saboda a samu rage Cunkoso a gidajen Yari.
Kazalika, ya ce Dakatar da Dokar, yana cikin kundin tsarin Mulkin Kasa na shekarar 1999, wanda aka yi masa Kwaskwarima.