Majalissar kasar nan ta sake maidawa karamin ministan kwadago, ayyuka da aikin yi Mr Festus Keyamo martani, inda ta bayyana cewa ministan bai’san banbancin dake tsakanin kishin kasa da shugabanci ba.
Kafin hakan dai an bayyana cewa a ranar talata data gabata ne ministan yaki ya nemi afuwar majalissar saboda ya daga musu murya a zuwansa majalissar domin yin bayani kan shirin Gwamnatin tarayya na daukar mutane Dubu 774 a wani sabon tsarin da take kokarin farawa a fadin kasar nan.
- Sanata Shehu Buba zai horas da matasa 250 kan sana’ar gyaran takalma a jihar Bauchi
- Cibiyoyin kula da lafiyar kafafu da hannaye a Najeriya ta bude sabon ofishi a Kano
- Gwamnan Namadi ya amince da Mai Martaba Sarkin Kazaure a matsayin Amirul Hajj na jihar Jigawa
- Dalibai 41,000 da ba su kai shekara 16 ba sun yi rajistar JAMB ta shekarar 2025
- Za a fara gudanar da jarrabawar WAEC da NECO ta hanyar na’ura wato CBT
Inda daga bisani a ranar larabar data gabata majalissar ta bayyana kin amincewarta da tsarin saboda rashin yi musu cikakken bayani.
Yayin zantawa da manena labarai a jiya Juma’a shugaban kwamitin yada labarai na majalissar Mr Benjamin Kalu, ya bayyana cewa majalissar ta fiskanci cewa majallisar zartarwar na kokarin nuna musu cewa basu san aikin su ba.

Sannan ya kara da cewa samun Baraka tsakanin turakunan Gwamnatin guda 3 zai iya haifar da koma bawa wajan ci gaban al’umma. Sannan ya kara da cewa fahimtar junansu zai taimakawa kasar nan.