Shugaban Karamar Hukumar, Hudu Babangida Dambazau wanda ya bayyana haka ga manema labarai a garin Gantsa, ya ce garuruwan da ambaliyar tafi kamari sune, Gantsa da Shawu da Buji da Matikir da Tsamfau da kuma Kukuma.
Babangida Dambazau wanda ya sami wakilcin mataimakin sa, Ahmed Zubairu, ya ce kayayyakin amfanin gona da suka lalace sun hadar da gero da dawa da wake da rogo da kuma shinkafa.
- Gwamnatin Sokoto Ta Bai Wa Sojojin Najeriya Gudummuwar Motocin Sulke 62
- Guguwar Iska Ta Kashe Mutane Uku, Ta Lalata Gidaje Da Ababen More Rayuwa A Yobe
- Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Takwas, Sun Kwato Makamai A Katsina
- Gwamnan Zamfara: Na Ƙi Biyan Kuɗin Fansa Naira Miliyan 300, Na Ce Su Kashe ‘Yan Uwana
- EFCC Ta Gurfanar da Bello Bodejo Kan Zargin Badaƙalar Kuɗi
Ya kara da cewa ambaliyar ta lalata hanyar da ta tashi daga Gantsa zuwa Tsamfau.
A jawabin sa, mai magana da yawun al’ummomin da ambaliyar ta shafa, Nazifi Garba ya roki gwamnatin tarayya da ta jiha da kuma ta karamar hukuma da sauran masu hannu da shuni su kai musu daukin gaggawa.