Shugaban Karamar Hukumar, Hudu Babangida Dambazau wanda ya bayyana haka ga manema labarai a garin Gantsa, ya ce garuruwan da ambaliyar tafi kamari sune, Gantsa da Shawu da Buji da Matikir da Tsamfau da kuma Kukuma.
Babangida Dambazau wanda ya sami wakilcin mataimakin sa, Ahmed Zubairu, ya ce kayayyakin amfanin gona da suka lalace sun hadar da gero da dawa da wake da rogo da kuma shinkafa.
- Airtel ta dakatar da bayar da bashin kati da data a Najeriya
- ’Yan adawa ba su isa su razanar da ni ba – Tinubu
- Sojoji sun kama masu satar man fetur a Legas, sun kama mutum 14
- Talauci ya ragu daga kaso 91 zuwa 41 a jihar Sokoto
- Bayan shekaru 12 da sace ɗaliban Chibok 272, har yanzu ba a san makomar 83 ba
Ya kara da cewa ambaliyar ta lalata hanyar da ta tashi daga Gantsa zuwa Tsamfau.
A jawabin sa, mai magana da yawun al’ummomin da ambaliyar ta shafa, Nazifi Garba ya roki gwamnatin tarayya da ta jiha da kuma ta karamar hukuma da sauran masu hannu da shuni su kai musu daukin gaggawa.