Shugaban Karamar Hukumar, Hudu Babangida Dambazau wanda ya bayyana haka ga manema labarai a garin Gantsa, ya ce garuruwan da ambaliyar tafi kamari sune, Gantsa da Shawu da Buji da Matikir da Tsamfau da kuma Kukuma.
Babangida Dambazau wanda ya sami wakilcin mataimakin sa, Ahmed Zubairu, ya ce kayayyakin amfanin gona da suka lalace sun hadar da gero da dawa da wake da rogo da kuma shinkafa.
- Ana ci gaba da kaɗa ƙuri’a a zaben shugaban kasar Chadi
- An kashe ‘yan ta’adda da dama a hare-haren da jiragen yaki suka kai a Borno da Nijar
- Ministan Shari’a ya yi alkawarin sake duba dokar da ta haramta yunkurin kunar bakin wake a Najeriya
- Cibiyar ICAN ta karrama Gwamna Mallam Umar Namadi na Jihar Jigawa da lambar yabo
- Abba Kabir Yusuf ya musanta korar masu aikin tsaftace titi a jihar Kano
Ya kara da cewa ambaliyar ta lalata hanyar da ta tashi daga Gantsa zuwa Tsamfau.
A jawabin sa, mai magana da yawun al’ummomin da ambaliyar ta shafa, Nazifi Garba ya roki gwamnatin tarayya da ta jiha da kuma ta karamar hukuma da sauran masu hannu da shuni su kai musu daukin gaggawa.