

Shugaban Karamar Hukumar, Hudu Babangida Dambazau wanda ya bayyana haka ga manema labarai a garin Gantsa, ya ce garuruwan da ambaliyar tafi kamari sune, Gantsa da Shawu da Buji da Matikir da Tsamfau da kuma Kukuma.
Babangida Dambazau wanda ya sami wakilcin mataimakin sa, Ahmed Zubairu, ya ce kayayyakin amfanin gona da suka lalace sun hadar da gero da dawa da wake da rogo da kuma shinkafa.
- Shugaba Buhari a ya jaddada kudirin gwamnatinsa na inganta rayuwar ‘yan Najeriya duk da mummunan yanayi na zamantakewa da tattalin arziki
- ‘Yan bindiga sun kashe jami’in Hukumar Shige da fice ta kasa 1 tare da raunata wasu 2 a karamar hukumar Birniwa
- Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta dakile wani yunkurin yin garkuwa da dagaci
- The National Bureau of Statistics says the aggregate production of mineral products in Nigeria grew from 64.29 million tons in 2020 to 89.48 million tons in 2021
- Shugaban Kasa Buhari ya taya murna ga ministan sadarwa bisa karrama a matsayin zama cikakken dan cibiyar tsaron hanyoyin sadarwa
Ya kara da cewa ambaliyar ta lalata hanyar da ta tashi daga Gantsa zuwa Tsamfau.
A jawabin sa, mai magana da yawun al’ummomin da ambaliyar ta shafa, Nazifi Garba ya roki gwamnatin tarayya da ta jiha da kuma ta karamar hukuma da sauran masu hannu da shuni su kai musu daukin gaggawa.