Shugaban kasar yayi kira ga masu ruwa da tsaki a zaben da za a gudanar a gobe Asabar da su kauracewa abinda ya kira, ko a mutu ko ayi rai.
Matsayar Shugaba Buhari na kunshe cikin wata sanarwa wacce kakakinsa, Garba Shehu, ya fitar.
- Kananun yara 5 ne suka mutu sakamakon rashin iska a cikin motar da suka makale a jihar Neja
- Yan sanda a Jihar Kaduna sun kama wani babban mai sayar wa ’yan bindiga makamai
- ‘Yan bindiga da ke addabar al’umma sun ajiye makamansu bayan wata tattaunawar sulhu
- Bobrisky ya ɗaukaka ƙara domin ƙalubalantar hukuncin kotun da ta aike dashi gidan gyaran hali
- Kwamitin majalisar dattawa kan wutar lantarki ya gayyaci Ministan Lantarki na kasa
Garba Shehu ya rawaito Buhari yana cewa ya jajirce matuka akan gudanar da zaben gaskiya da adalchi, amma jajircewarsa baza ta isa ba muddin masu aikin zaben suka ki kiyayewa da dokoki.
Shugaban kasar ya kara da cewa yana so yaga an dabbaka tsarin demokradiyya a kasarnan.