Ruwan sama kamar da bakin kwarya ya lalata wani bangare na cibiyar lafiya ta garin Saleri dake yankin karamar Hukumar Kirikasamma anan jihar Jigawa.
Manajan Hukumar lafiya matakin farko na yankin Usman Abdullahi Birniwa ya sanar da hakan ga manema labarai a Birniwa.
Yace ruwan saman hade da iska ya lalata sashen kula da mata masu juna biyu da kuma wasu kayayyakin aiki.
- Gwamnan jihar Kogi ya nemi gwamnatin tarayya da ta taimakawa jihar wajen yaki da matsalar tsaro da ambaliyar ruwa
- An kama wasu mutane biyu da ake zargi da laifin fasa kwaurin wutar lantarki a jihar Katsina
- Hukumar Kwastam ta kama shinkafar kasar waje guda 212 wanda kudinsu ya haura N126m
- Daniel Bwala mai magana da yawun Atiku Abubakar ya caccaki Hukumar EFCC
- An kama wasu masu garkuwa da mutane uku a yankin Lankaviri dake jihar Taraba
Usman Abdullahi yace a yanzu haka ambaliyar ruwa na neman mamaye cibiyar lafiyar inda ya roki gwamnati data kai musu daukin gaggawa.
Tunda farko kamsilan sashen tsare tsare Abdullahi Gada yace karamar hukumar ta bada gudunmawar fatun bahuna 200 domin yin jinga a cibiyar.
Ambaliyar ruwa ta lalata gidaje 46 yayin da kayayyakin amfanin gona na miliyoyin naira suka salwanta a garin na Saleri.