Majalissar zartarwa ta Jihar Jigawa ta amince da fitar da kudi sama da naira miliyan 194 domin gudanar da karin ayyukan magance zaizayar kasa da ambaliyar ruwa a wajen da ake gina sabon asibitin kwararru na Kazaure.
Kwamishinan yada labarai matasa da wasanni na jiha Alhaji Bala Ibrahim Mamsa ya sanar da hakan bayan zaman majalisar da Gwamna Muhammad Badaru Abubakar ya jagoranta.
- Kananun yara 5 ne suka mutu sakamakon rashin iska a cikin motar da suka makale a jihar Neja
- Yan sanda a Jihar Kaduna sun kama wani babban mai sayar wa ’yan bindiga makamai
- ‘Yan bindiga da ke addabar al’umma sun ajiye makamansu bayan wata tattaunawar sulhu
- Bobrisky ya ɗaukaka ƙara domin ƙalubalantar hukuncin kotun da ta aike dashi gidan gyaran hali
- Kwamitin majalisar dattawa kan wutar lantarki ya gayyaci Ministan Lantarki na kasa
Ibrahim Mamsa yayi bayanin cewa majalisar ta amince da karin ayyukan ne sakamakon rahotan data samu wanda ke nuni da cewar zaizayar kasa da ambaliyar ruwa na barazana ga aikin gina asibitin.
Kwamishinan ya cigaba da cewa tun farko an bada kwangilar aikin ne akan kudi naira biliyan dubu 1 da miliyan 893.