

Kungiyar kwadago ta NLC ta yi barazanar tsayar duk wata hada-hadar tattalin arziki, muddin gwamnatin tarayya ta ki janye karin kudin man fetur da na wuta, cikin kwanaki goma sha hudu.
Shugaban kungiyar na kasa, Ayuba Wabba, ya sanar da haka a karshen zaman kwamitin aikin kungiyar na kasa, wanda aka gudanar jiya a Abuja.
- Tarihin Gamuwa 10 Tsakanin Kano Pillars VS Eyimba Da Kuma Wasan Yau
- Abubuwa 5 da suka zama wajibi lokacin sanyi
- An ƙaddamar da kudin kariya ga ƴan jarida da masu fafutukar ƴancin amfani da yanar gizo
- Yadda ake duba suna don zama ma’aikacin damara na 2020 a Nijeria
- Me Ƙungiyar Izala ta ce kan matsalolin tsaro a Najeriya?
- Muhimmiyar shawara ga manoma kan Noman rani
Ayuba Wabba yace ma’aikata da sauran yan Najeriya sun shiga damuwa kan yadda gwamnati ta yanke shawarar kara kudin man fetur da na wuta, a daidai lokacin da sauran kasashe a fadin duniya ke kokarin saukawawa mutanensu wahalhalun rayuwa domin rage illar annobar corona.
A cewar Ayuba Wabba, kwamitin aikin kungiyar na kasa ya gano cewa annobar corona da matsin tattalin arzikin da kasa ke ciki ya jawowa yan Najeriya wahalhalu da dama, kuma a yanzu karin farashin ya sake tagayyara su.