Kungiyar kwadago ta NLC ta yi barazanar tsayar duk wata hada-hadar tattalin arziki, muddin gwamnatin tarayya ta ki janye karin kudin man fetur da na wuta, cikin kwanaki goma sha hudu.
Shugaban kungiyar na kasa, Ayuba Wabba, ya sanar da haka a karshen zaman kwamitin aikin kungiyar na kasa, wanda aka gudanar jiya a Abuja.
- ‘Yan bindiga sun kashe babban limamin masallacin Juma’a na kauyen Keita
- Gobara ta ƙone motoci da rumfunan katako takwas da kuma kayan aikin kafinta ƙurmus
- Kwamitin Masallacin Dutse ya raba buhunan Shinkafa buhu 30,000 ga zawarawa da sauran marasa galihu
- Kwamandojin Boko Haram biyu sun mika wuya ga sojojin rundunar hadin gwiwa ta MNJTF
- Dan takarar jam’iyyar adawa Bassirou Diomaye Faye ne ke kan gaba a zaben shugaban kasar Senegal
- Gwamnan jihar Borno Babagana Zulum ya nada mataimaka 168 da membobin gudanarwa 104
Ayuba Wabba yace ma’aikata da sauran yan Najeriya sun shiga damuwa kan yadda gwamnati ta yanke shawarar kara kudin man fetur da na wuta, a daidai lokacin da sauran kasashe a fadin duniya ke kokarin saukawawa mutanensu wahalhalun rayuwa domin rage illar annobar corona.
A cewar Ayuba Wabba, kwamitin aikin kungiyar na kasa ya gano cewa annobar corona da matsin tattalin arzikin da kasa ke ciki ya jawowa yan Najeriya wahalhalu da dama, kuma a yanzu karin farashin ya sake tagayyara su.