Gwamnatin Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ta amince da kafa wata sabuwar hukuma da zata yaki cin hanci da rashawa.
Sabuwar hukumar wacce majalisar zartarwa ta tarayya ta amince da ita, za a dora mata nauyin kula da dukkan kadarorin satar da aka kwato.
Ministan shari’ah kuma babban lauyan tarayya, Abubakar Malami, ya sanar da haka ga manema labaran fadar shugaban kasa, bayan zaman ganawar majalisar zartarwa ta tarayya wanda aka gudanar a jiya laraba.
- ‘Yan bindiga da ke addabar al’umma sun ajiye makamansu bayan wata tattaunawar sulhu
- Bobrisky ya ɗaukaka ƙara domin ƙalubalantar hukuncin kotun da ta aike dashi gidan gyaran hali
- Kwamitin majalisar dattawa kan wutar lantarki ya gayyaci Ministan Lantarki na kasa
- Mutum takwas sun mutu a hatsarin mota a jihar Kogi
- An sallami wasu sojoji daga aiki bisa yin wata gagarumar sata a matatar manfetur ta Dangote
Yace sabuwar hukumar za ta sake bibiyar yadda ake kula da kadarori da dukiyoyin da aka kwato daga hannun marasa gaskiya.
Ministan yace majalisar zartarwa ta tarayya ta amince da aikawa da kudirin neman kafa hukumar zuwa ga majalisar kasa.