

Sarkin Kano, Mai Martaba Alhaji Aminu Ado Bayero, ya yabawa gwamna Muhammadu Badaru Abubakar bisa aiwatar da ayyukan raya kasa a jihar Jigawa.
Ya sanar da haka lokacin da ya kaiwa gwamnan ziyara a gidan gwamnatin dake Dutse.
Sarkin ya bayyana cewa yayin ziyararsa zuwa masarautun jiharnan, ya yaba da ayyukan da suka kawata birane da yankunan karkara a fadin jihar.
- Kuji tsoron Allah ko koma gare Shi, Atiku yayi kira ga yan Najeriya.
- Goodluck Jonathan: Kuri’un talakawa ya kamata su tattance zabe ba kotu ba
- Sarkin musulmi: Gobe Talata shine daya ga watan Ramadan
- Kamfanin Twitter zai kafa reshe a Afirka
- Kungiyar Barcelona ta fi ko wacce kungiya kudi a duniya
- Dalibai da yawa zasu rasa damar rubuta JAMB ta bana a Najeriya
Aminu Ado Bayero ya gayawa gwamnan cewa yazo jihar ne domin gabatar da kansa tare da neman shawarwarin sarakunan, inda ya godewa mutanen jiharnan bisa kyakykyawar tarbar da suka yi masa.
Da yake mayar da martani, Gwamna Badaru Abubakar yace yayi farinciki da alfahari da ziyarar sarkin, wacce yace zata karfafa danganta mai kyau da tarihi tsakanin mutanen jihoshin Kano da Jigawa.