Hukumar Jiragen Kasa ta Najeriya ta musanta rahotannin da ke zargin cewa mahara sun kai hari kan jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna a shekaranjiya Litinin da rana.
Manajan Darakta na hukumar, Fidet Okiriya, wanda ya musanta hakan cikin wata sanarwa, yace rahotannin, kanzon kurege ne.
A cewarsa, akwai wasu bata gari wadanda suke yawan jefa manyan duwatsu kan jirgin kasa dake tafiya akan hanyar Abuja zuwa Kaduna.
- ‘Yan bindiga sun kashe babban limamin masallacin Juma’a na kauyen Keita
- Gobara ta ƙone motoci da rumfunan katako takwas da kuma kayan aikin kafinta ƙurmus
- Kwamitin Masallacin Dutse ya raba buhunan Shinkafa buhu 30,000 ga zawarawa da sauran marasa galihu
- Kwamandojin Boko Haram biyu sun mika wuya ga sojojin rundunar hadin gwiwa ta MNJTF
- Dan takarar jam’iyyar adawa Bassirou Diomaye Faye ne ke kan gaba a zaben shugaban kasar Senegal
Sai dai, ya bukaci masu amfani da jiragen kasan da kada su razana, kasancewar ministan sufuri da hukumar jiragen kasa zasu tabbatar da tsaron lafiyar yan Najeriya akan hanyar.
Kazalika, manajan sufurin jiragen kasan Abuja zuwa Kaduna, Faskal Norli, ya tabbatar da cewa jirgin kasan ya isa tashar Idu a ranar Litinin kamar yadda aka tsara, kuma ya musanta duk wani hari daga mahara.