Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki Shiyyar Kano (KEDCO) yace ya dauki matakan da suka kamata wajen kawo karshen korafe-korafen masu sabuwar mita da ake saka mata kati.
Jihoshin dake karkashin KEDCO sune Jigawa da Kano da Katsina.
Shugaban Sashen Yada Labarai na Kamfanin, Ibrahim Shawai, ya sanar da hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a Kano.
- Tsananin zafi yasa an rufe daukacin makarantun dake kasar Sudan ta kudu
- An sake sassauta dokar hana zirga-zirgar babura masu kafa uku a wasu sassan jihar Adamawa
- Sanata Abdul’Aziz Yari ya bukaci al’ummar Musulmi da su yi amfani da lokacin Ramadan wajen yi wa Shugaba Bola Tinubu addu’a
- Wasu ‘yan bindiga sun yi garkuwa da mutane 14 a kauyen Dogon Noma-Ungwan Gamo
- Dan majalisa mai wakiltar mazabar Kaga da Magumeri da Gubio a majalisar wakilai ya raba kayan abinci ga iyalai 5,000
Ibrahim Shawai ya sanar da cewa kamfanin ya dauki matakan inganta ayyukansa domin magance yawan korafe-korafe akan sabuwar mitar.
Yayi nuni da cewa an samu jan kafa wajen fara aiwatar da sabon kudin wuta kasancewar masu sabuwar mitar sun ki amincewa da katin wutar da suka saya farawa daga ranar 1 ga watan Satumba.
Yace kamfanin ya bayar da muhimmanci wajen magance korafe-korafen da suka shafi mita, domin biyan bukatar abokan hulda.