Masu ruwa da tsakin jam’iyyar APC a jihar Yobe sun bukaci majalisar dokokin jihar da ta tsige gwamna Mai Mala Buni, wanda shi ne shugaban riko na jam’iyyar ta kasa, muddin ya gaza yin murabus.
Sun alakanta bukatar ne da gazawar gwamnan wajen sauke nauyin dake wuyansa, kamar yadda kundin tsarin mulkin kasa ya tanadar a matsayinsa na gwamna.
- Shugaba Tinubu ya umarci duka hukumomin gwamnati da su sayi motoci masu amfani da iskar gas
- Akalla mutane 24 ne suka mutu sanadiyyar wani gini da ya ruguje a ƙasar Afrika ta Kudu
- Rundunar tsaro ta hadin gwiwa ta kubutar da wasu fasinjoji 17 da aka sace a jihar Katsina
- EFCC ta kama wasu mutane 26 da ake zargi da damfara ta intanet a jihar Ribas
- Wata Kungiya mai zaman kanta ta yi aikin jinya ga mata manoma 200 a jihar Jigawa
Masu ruwa da tsakin sun zargin gwamna Buni, da yin shakulatin bangaro da lamurran jihar kacokan, inda yakan ziyarci jihar akalla sau guda cikin tsawon wata 1.
Sun bayyana bukatar ne cikin wata sanarwa da suka fitar bayan wani taro da suka gudanar a Abuja.
Sun ce an zabi Buni ne a matsayin gwamnan jihar ba wai shugaban jam’iyya ba, kuma yasha rantsuwar yin biyayya ga kundin tsarin mulkin kasa, to sai dai a yanzu, yayi watsi da al’umarsa a lokacin da suke bukatarsa.