Masu ruwa da tsakin jam’iyyar APC a jihar Yobe sun bukaci majalisar dokokin jihar da ta tsige gwamna Mai Mala Buni, wanda shi ne shugaban riko na jam’iyyar ta kasa, muddin ya gaza yin murabus.
Sun alakanta bukatar ne da gazawar gwamnan wajen sauke nauyin dake wuyansa, kamar yadda kundin tsarin mulkin kasa ya tanadar a matsayinsa na gwamna.
- Barcelona ta ba Lamine Yamal lamba 10
- An ɗaura auren Umaru Musa Yar’Adua Jnr., ɗan marigayi tsohon shugaban ƙasa, Alhaji Umaru Musa Yar’Adua, tare da amaryarsa Maryam Ayuba Shuaibu
- Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Alhaji Atiku Abubakar (GCON), ya kawo karshen shakku da tsokaci, inda a hukumance ya fice dga jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP),
- Manhajar TikTok ta goge fiye da bidiyo miliyan 3.6 a Najeriya saboda saba ka’idar dokokinta
- Tsohon Shugaban APC na ƙasa kuma tsohon Gwamnan Jihar Edo, ya fice daga jam’iyya APC zuwa jam’iyyar hadaka ta ADC
Masu ruwa da tsakin sun zargin gwamna Buni, da yin shakulatin bangaro da lamurran jihar kacokan, inda yakan ziyarci jihar akalla sau guda cikin tsawon wata 1.
Sun bayyana bukatar ne cikin wata sanarwa da suka fitar bayan wani taro da suka gudanar a Abuja.
Sun ce an zabi Buni ne a matsayin gwamnan jihar ba wai shugaban jam’iyya ba, kuma yasha rantsuwar yin biyayya ga kundin tsarin mulkin kasa, to sai dai a yanzu, yayi watsi da al’umarsa a lokacin da suke bukatarsa.